• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 2 Sun Mutu, An Ceto 5 Yayin Da Gini Ya Rufta A Abuja

by Sadiq
3 years ago
Abuja

Mazauna yankin Kubwa da ke babban birnin tarayya, Abuja sun shiga firgici bayan da wani bene mai hawa biyu ya ruguje wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu.

Ginin wanda ake kan gina shi ya ruguje ne a titin Hamza Abdullahi da ke kan titin Gado Nasco.

  • Abin Da Ya Sa Ba A Son Yin Wanka In Ana Ruwa Da Walkiya A Birtaniya
  • Zulum Ya Ba Da Umarnin Bude Ofishin NNPP Da Aka Rufe A Borno

Jami’an Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) na ta aikin ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

A cewar NEMA, mutane shida ne lamarin ya rutsa da su.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce NEMA ta sanar da faruwar lamarin da misalin karfe 1:00 na rana, inda nan take ta tattara wadanda suka kai daukin gaggawa, wadanda suka hada da hukumar bayar da agajin gaggawa ta Abuja, hukumar kashe gobara, jami’an tsaron farin kaya da kuma ‘yansanda zuwa wurin.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Babban Birnin Tarayya Abuja (FEMA), Alhaji Abbas Idris, ya sanar a jiya cewa mutane biyu da suka makale a ginin da ya ruguje a Kubwa da ke wajen birnin Abuja, sun mutu.

Alhaji Idriss, ya ce aikin ceto a wurin da ya rufta ya zo karshe tare da ceto mutane biyar da ransu; uku da suka samu raunuka daban-daban yayin da mutane biyu ba su samu raunuka ba.

A halin da ake ciki, karamar ministar babban birnin tarayya Abuja, Dakta Ramatu Tijjani Aliyu, ta jajanta wa iyalan wadanda ginin Kubwa ya shafa.

Hafeez Olayinka, daya daga cikin wadanda aka ceto daga ginin da ya rufta, ya ce ya shafe sa’o’i a cikin tarko.

Olayinka, wanda ya koma inda lamarin ya faru bayan an yi masa jinya a asibiti, ya shaida wa manema labarai cewa ya isa wurin ginin da ya ruguje ne a ranar Litinin.

“Ni da wasu mun makale tun daren Alhamis. Da misalin karfe 11:30 na dare ranar Alhamis.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
Manyan Labarai

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Next Post
Za A Hana ‘Yan Kasar Waje Sayen Amfanin Gona Kai-tsaye A Gonaki

Za A Hana 'Yan Kasar Waje Sayen Amfanin Gona Kai-tsaye A Gonaki

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.