• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

by Sadiq
15 hours ago
in Manyan Labarai
0
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aƙalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu a hare-haren ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

Ɗan majalisar jihar da ke wakiltar Malumfashi, Hon. Aminu Ibrahim, ya shaida wa majalisar dokokin jihar cewa ‘yan bindiga sun kashe mutane 30 da ke salla sannan suka ƙone mutane 20 da ransu a sabbin hare-haren da aka kai a ƙauyukan mazaɓarsa.

  • An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
  • Dole Ne Fasinjoji Su Kashe Wayoyinsu Gaba Ɗaya Kafin Jirgi Ya Tashi Ko Sauka – NCAA

Hare-haren sun faru ne a Gidan Adamu Mantau, Unguwar Yar Mai Dabo, Makera da kuma Burdigau.

Ibrahim ya ce lamarin ya bar jama’a cikin tsoro da baƙin ciki.

Ya bayyana cewa mazauna ƙauyukan sun yi kira da aka kai musu ɗauki kan hare-haren‘yan bindiga a kusa da Burdigau da misalin ƙarfe 6 zuwa 7 na yamma a ranar Litinin, amma sojoji sun iso daga baya suka kuma tafi ba tare da tsare yankin ba.

Labarai Masu Nasaba

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025

Da safiyar ranar Talata, sai ‘yan bindiga suka kai farmaki Unguwar Mantau tare da buɗe wasu mutane da ke sallar Asubah wuta, inda suka kashe mutum 30.

“Lamarin ya zama abun baƙin ciki. Mutanenmu ba za su iya ci gaba da rayuwa a ƙauyukansu ba saboda waɗannan hare-hare marasa ƙarewa,” in ji Ibrahim, yana roƙon a kafa sansanonin sojoji a Karfi da Yaba.

Jawabin nasa ya tayar da hankali a tsakanin sauran ‘yan majalisa, waɗanda suka nuna cewa kisan gilla yana ƙaruwa a Katsina duk da ayyukan da sojoji ke yi a jihar.

Mazauna Malumfashi sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su ɗauki matakin gaggawa.

A baya an tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kashe masallata 13 ne a Unguwar Mantau da safiyar ranar Talata.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya shaida wa ‘yan jarida cewa gwamnati ta bayar da umarnin ƙara tsaro tare da kai wa waɗanda abin ya shafa tallafi.

“Lamarin ya faru ne lokacin da miyagu suka kai harin ramuwar gayya kan al’umma. Mutane na unguwar suna cikin masallaci suna sallar Asuba lokacin da miyagun suka fara harbe-harbe a cikin masallaci,” in ji Dr. Mu’azu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariKatsinaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

Next Post

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

Related

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

12 hours ago
EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025

19 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Karbe Filin Jirgin Saman Gombe
Manyan Labarai

Dole Ne Fasinjoji Su Kashe Wayoyinsu Gaba Ɗaya Kafin Jirgi Ya Tashi Ko Sauka – NCAA

20 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Masallata 13 A Jihar Katsina

22 hours ago
NNPP Za Ta Iya Goyon Bayan Takarar Tinubu A 2027 – Sakataren Jam’iyyar
Manyan Labarai

NNPP Za Ta Iya Goyon Bayan Takarar Tinubu A 2027 – Sakataren Jam’iyyar

1 day ago
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna

2 days ago
Next Post
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al'adu Mai Taken "Sautin Zaman Lafiya" A Nairobi

LABARAI MASU NASABA

Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

August 20, 2025
Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

August 20, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Watsi Ga Ƙarin Girma Ga ASP 179, Ta Ɗaga Darajar 952 Zuwa DSP

August 20, 2025
Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani

Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani

August 20, 2025
Xi Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Yankin Xizang

Xi Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Yankin Xizang

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.