ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Xizang

Bana shekara ce ta cika shekaru 60 da kafuwar yankin Xizang mai cin gashin kansa na kasar Sin, lamarin da ya zama ba wai kawai lokacin biki ba ne, har ma da waiwaye adon tafiya kan wata turba ta ruhin samun ci gaba da sauye-sauye a yankin kudu maso yammacin kasar Sin. Xizang ya taba kasancewa wani yanki mai nisa dake cikin mawuyacin hali, amma a yanzu ya zama shaida kuma abin kwatance a bangaren juriya, da samun bunkasa da kuma farfado da raya al’adu.

 

A shekarar 1965, saboda yanayin muhallin yankin Xizang da rashin ababen more rayuwa da suka sada shi da sauran sassan kasar Sin, ya zama yanki mafi girma mai wahalar zuwa a duk fadin kasar. Hanyoyi sun yi karanci, kana mutanen yankin suna rayuwa ba tare da walwala ta a-zo-a-gani ba. Amma zuwa shekarar 2024, yankin ya samu lafiyayyun hanyoyi masu nisan kilomita 124,900, inda aka sada kauyuka da birane da juna. Layin dogo na Qinghai zuwa Xizang da zirga-zirgar jiragen sama 180 da ake yi sun mayar da yankin dake kan tudu mai tsawo da ya zama tamkar saniyar ware zuwa cibiyar hada-hada da samun damammaki.

ADVERTISEMENT
  • Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani
  • EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025

Bari mu dauki Kauyen Galai dake Nyingchi na Xizang domin buga misali a kan bunkasar tattalin arzikin yankin. A lokutan baya, kauyen ya dogara ne da noma na ciyar da iyali kawai, amma a yanzu ya shahara ta fuskar yawon bude ido da kuma kafuwar masana’antun inganta muhalli. Tattalin arzikin furen “peach,” wanda ake samu daga bishiyoyin kauyen masu dadadden tarihi da kyawawan wurare masu dausayi, sun zama wani tambari na farfadowar yankin karkara a duniya. Kudin shiga da aka kiyasta samu ga kowane mutum a Galai duk shekara ya zarce yuan 40,000 a shekarar 2024. Yanzu haka mazauna kauyen suna samun kudin shiga ta hanyoyi daban-daban, tun daga kan jigilar kayayyaki, hidimomin baki, da kuma hada-hadar gamayyar kungiyoyin yawon shakatawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Karfin tattalin arzikin yankin Xizang ya kai adadin kudin kasar Sin yuan biliyan 276.5 a shekarar 2024, wanda ya ninka sau 155 a kan na shekarar 1965, inda aka rika samun matsakaicin karuwarsa a mizanin shekara-shekara da kaso 8.9%, kana a bana da yankin ke cika shekaru 60 da kafuwa, ana sa ran karfin tattalin arzikin nasa zai haura yuan biliyan 300. Xizang ya samu wannan tagomashin ne daga sassan masana’antun makamashi mai tsafta, da aikin noma, da yawon bude ido a bangaren tarihi da al’adu, bisa goyon bayan kawancensa da wasu lardunan da suka ci gaba a karkashin tsarin ba da tallafi na kasar Sin.

 

Kazalika, Xizang ya samu ci gaban walwalar jama’a mai zurfi ta yadda mazaunansa ke more rayuwa irin na dan’adam mai ’yanci. An fadada samar da ingantattun harkokin kiwon lafiya da ilimi. An bude manyan tituna zuwa kananan gundumomi da ba a iya kaiwa a baya inda hakan ya kara kawo sauyi ga kula da ayyukan jama’a. Akwai makarantu, da asibitoci, da cibiyoyin koyar da sana’o’i a yankin na zamani, wanda hakan ya bai wa al’ummar Xizang ta yanzu damar yin amfani da kayan aikin da za su kara musu fahimtar albarkatun da suke da su.

 

A halin yanzu, Xizang ya zama daya daga cikin yankunan da ke da mafi kyawun yanayin muhalli a duniya. Kokarin da ake ta faman yi a tsakanin gwamnatin tsakiya da ta yankin ya kiyaye wurare masu tarihi na asali da bayar da damar samun ci gaba mai dorewa a karkashin falsafar “ruwan Lucid da tsaunukan lush dukiyoyi ne masu dimbin daraja.”

 

Bikin cika shekaru 60 na yankin Xizang mai cin gashin kansa ya zarce wata alama ta ci gaba, sai dai a ce wani madubi ne dake nuna yadda yankin ya yi fintikau ta fuskar samun bunkasa daga tsohon yanayinsa na tabarbarewar hanyoyi da rashin habakar tattalin arziki, sakamakon tsare-tsaren da aka yi amfani da su na hangen nesa, da shugabanci na-gari, da kuma karfin ruhin juriya na al’ummarsa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Xizang
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Xizang
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Sulaiman
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

MASU ALAKA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
Daga Birnin Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
Daga Birnin Sin

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Next Post
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

LABARAI MASU NASABA

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.