ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

by Sadiq
10 months ago
Katsina

Aƙalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu a hare-haren ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

Ɗan majalisar jihar da ke wakiltar Malumfashi, Hon. Aminu Ibrahim, ya shaida wa majalisar dokokin jihar cewa ‘yan bindiga sun kashe mutane 30 da ke salla sannan suka ƙone mutane 20 da ransu a sabbin hare-haren da aka kai a ƙauyukan mazaɓarsa.

  • An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
  • Dole Ne Fasinjoji Su Kashe Wayoyinsu Gaba Ɗaya Kafin Jirgi Ya Tashi Ko Sauka – NCAA

Hare-haren sun faru ne a Gidan Adamu Mantau, Unguwar Yar Mai Dabo, Makera da kuma Burdigau.

ADVERTISEMENT

Ibrahim ya ce lamarin ya bar jama’a cikin tsoro da baƙin ciki.

Ya bayyana cewa mazauna ƙauyukan sun yi kira da aka kai musu ɗauki kan hare-haren‘yan bindiga a kusa da Burdigau da misalin ƙarfe 6 zuwa 7 na yamma a ranar Litinin, amma sojoji sun iso daga baya suka kuma tafi ba tare da tsare yankin ba.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Da safiyar ranar Talata, sai ‘yan bindiga suka kai farmaki Unguwar Mantau tare da buɗe wasu mutane da ke sallar Asubah wuta, inda suka kashe mutum 30.

“Lamarin ya zama abun baƙin ciki. Mutanenmu ba za su iya ci gaba da rayuwa a ƙauyukansu ba saboda waɗannan hare-hare marasa ƙarewa,” in ji Ibrahim, yana roƙon a kafa sansanonin sojoji a Karfi da Yaba.

Jawabin nasa ya tayar da hankali a tsakanin sauran ‘yan majalisa, waɗanda suka nuna cewa kisan gilla yana ƙaruwa a Katsina duk da ayyukan da sojoji ke yi a jihar.

Mazauna Malumfashi sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su ɗauki matakin gaggawa.

A baya an tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kashe masallata 13 ne a Unguwar Mantau da safiyar ranar Talata.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya shaida wa ‘yan jarida cewa gwamnati ta bayar da umarnin ƙara tsaro tare da kai wa waɗanda abin ya shafa tallafi.

“Lamarin ya faru ne lokacin da miyagu suka kai harin ramuwar gayya kan al’umma. Mutane na unguwar suna cikin masallaci suna sallar Asuba lokacin da miyagun suka fara harbe-harbe a cikin masallaci,” in ji Dr. Mu’azu.

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al'adu Mai Taken "Sautin Zaman Lafiya" A Nairobi

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.