• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Xizang

Bana shekara ce ta cika shekaru 60 da kafuwar yankin Xizang mai cin gashin kansa na kasar Sin, lamarin da ya zama ba wai kawai lokacin biki ba ne, har ma da waiwaye adon tafiya kan wata turba ta ruhin samun ci gaba da sauye-sauye a yankin kudu maso yammacin kasar Sin. Xizang ya taba kasancewa wani yanki mai nisa dake cikin mawuyacin hali, amma a yanzu ya zama shaida kuma abin kwatance a bangaren juriya, da samun bunkasa da kuma farfado da raya al’adu.

 

A shekarar 1965, saboda yanayin muhallin yankin Xizang da rashin ababen more rayuwa da suka sada shi da sauran sassan kasar Sin, ya zama yanki mafi girma mai wahalar zuwa a duk fadin kasar. Hanyoyi sun yi karanci, kana mutanen yankin suna rayuwa ba tare da walwala ta a-zo-a-gani ba. Amma zuwa shekarar 2024, yankin ya samu lafiyayyun hanyoyi masu nisan kilomita 124,900, inda aka sada kauyuka da birane da juna. Layin dogo na Qinghai zuwa Xizang da zirga-zirgar jiragen sama 180 da ake yi sun mayar da yankin dake kan tudu mai tsawo da ya zama tamkar saniyar ware zuwa cibiyar hada-hada da samun damammaki.

  • Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani
  • EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025

Bari mu dauki Kauyen Galai dake Nyingchi na Xizang domin buga misali a kan bunkasar tattalin arzikin yankin. A lokutan baya, kauyen ya dogara ne da noma na ciyar da iyali kawai, amma a yanzu ya shahara ta fuskar yawon bude ido da kuma kafuwar masana’antun inganta muhalli. Tattalin arzikin furen “peach,” wanda ake samu daga bishiyoyin kauyen masu dadadden tarihi da kyawawan wurare masu dausayi, sun zama wani tambari na farfadowar yankin karkara a duniya. Kudin shiga da aka kiyasta samu ga kowane mutum a Galai duk shekara ya zarce yuan 40,000 a shekarar 2024. Yanzu haka mazauna kauyen suna samun kudin shiga ta hanyoyi daban-daban, tun daga kan jigilar kayayyaki, hidimomin baki, da kuma hada-hadar gamayyar kungiyoyin yawon shakatawa.

 

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Karfin tattalin arzikin yankin Xizang ya kai adadin kudin kasar Sin yuan biliyan 276.5 a shekarar 2024, wanda ya ninka sau 155 a kan na shekarar 1965, inda aka rika samun matsakaicin karuwarsa a mizanin shekara-shekara da kaso 8.9%, kana a bana da yankin ke cika shekaru 60 da kafuwa, ana sa ran karfin tattalin arzikin nasa zai haura yuan biliyan 300. Xizang ya samu wannan tagomashin ne daga sassan masana’antun makamashi mai tsafta, da aikin noma, da yawon bude ido a bangaren tarihi da al’adu, bisa goyon bayan kawancensa da wasu lardunan da suka ci gaba a karkashin tsarin ba da tallafi na kasar Sin.

 

Kazalika, Xizang ya samu ci gaban walwalar jama’a mai zurfi ta yadda mazaunansa ke more rayuwa irin na dan’adam mai ’yanci. An fadada samar da ingantattun harkokin kiwon lafiya da ilimi. An bude manyan tituna zuwa kananan gundumomi da ba a iya kaiwa a baya inda hakan ya kara kawo sauyi ga kula da ayyukan jama’a. Akwai makarantu, da asibitoci, da cibiyoyin koyar da sana’o’i a yankin na zamani, wanda hakan ya bai wa al’ummar Xizang ta yanzu damar yin amfani da kayan aikin da za su kara musu fahimtar albarkatun da suke da su.

 

A halin yanzu, Xizang ya zama daya daga cikin yankunan da ke da mafi kyawun yanayin muhalli a duniya. Kokarin da ake ta faman yi a tsakanin gwamnatin tsakiya da ta yankin ya kiyaye wurare masu tarihi na asali da bayar da damar samun ci gaba mai dorewa a karkashin falsafar “ruwan Lucid da tsaunukan lush dukiyoyi ne masu dimbin daraja.”

 

Bikin cika shekaru 60 na yankin Xizang mai cin gashin kansa ya zarce wata alama ta ci gaba, sai dai a ce wani madubi ne dake nuna yadda yankin ya yi fintikau ta fuskar samun bunkasa daga tsohon yanayinsa na tabarbarewar hanyoyi da rashin habakar tattalin arziki, sakamakon tsare-tsaren da aka yi amfani da su na hangen nesa, da shugabanci na-gari, da kuma karfin ruhin juriya na al’ummarsa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Daga Birnin Sin

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Next Post
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.