• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

A jiya Laraba 3 ga wata, kasar Sin ta gudanar da kasaitaccen bikin faretin soja a birnin Beijing, don tunawa da cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan da ma yakin duniya da tafarkin murdiya, bikin da ya jawo hankalin duniya, har ma wasu abokaina ‘yan Nijeriya sun turo min sakonni, inda suka ce su ma sun kalli gaba dayan bikin, kuma suna mai jinjinawa ga kasar Sin, musamman ganin yadda ta bunkasa har ta zama kasa mai karfin tattalin arziki ta biyu a duniya, bayan yadda ta kasance kasar da aka kai mata hari tare da mamaya a baya. A wata makala da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya wallafa a shafinsa, ya yi nuni da cewa, kwarin gwiwar da jama’ar kasar Sin suka samu daga yaki da maharan kasar Japan ya zama arziki gare su, wanda ya ke matsa musu kaimin tinkarar matsalolin da wahalhalun da ke gabansu, don cimma burin zamanantar da kasarsu da farfado da al’ummun kasar.

Na kuma lura da cewa, shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da shugaban jamhuriyar Congo Denis Sassou Nguesso sun zo kasar Sin don halartar bikin. Kafin ya tashi zuwa kasar Sin, shugaba Sassou ya bayyana cewa, nasarar yakin duniya da tafarkin murdiya ta dogara ne da kokarin da dukkanin al’ummomin duniya masu kishin zaman lafiya da adalci suka yi, idan har masu bin tafarkin murdiya suka cimma nasarar yakin a lokacin, lallai da wuya mu yi zaton irin duhun da dan Adam zai shiga. Ya ce, al’ummar kasar Sin sun bayar da muhimmiyar gudummawa ga cimma nasarar yakin, a yayin da al’ummun kasashen Afirka da dama ma suka sadaukar da rayukansu a yakin, wadanda suka ketare hamadar Sahara da Bahar Rum, suka shiga yakin kafada da kafada tare sojojin kasashen kawance. Abin haka yake, yakin da aka yi da tafarkin murdiya a shekaru 80 da suka wuce, ya kasance turjiyar al’ummomin kasashen duniya, ciki har da na kasar Sin da kasashen Afirka, ga hari da zaluncin mulkin danniya, wanda hakan ya zama nasarar masu kishin adalci da zaman lafiya.

A ganina, dalilin da ya sa bikin tunawa da nasarar da kasar Sin ta shirya ya burge bangarori daban daban na kasashen Afirka, shi ne sabo da abubuwa kusan iri daya ne suka faru a gare su a tarihi, wato dukkansu sun taba fuskantar mamayar mahara da ma mulkin mallaka da aka yi musu, kuma suka samu ‘yancin kansu bisa ga fafatawar da suka yi, har wa yau kuma, dukkansu suna da burin tabbatar da ci gabansu da ma farfado da al’ummunsu. Sakamakon hakan kuma, sun fi fahimta da kishin zaman lafiya da ci gaba.

Sai dai ko da yake tuni zaman lafiya da ci gaba sun zama jigon zamanin da muke ciki, amma har yanzu akwai rina a kaba, inda ake ta kara fuskantar matsalolin daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da nuna fin karfi a duniya, kuma zaman lafiya ko yaki, yin shawarwari da juna ko yin fito na fito da juna, cin moriyar juna ko cin nasara daga faduwar wani bangare, ya zama sabon zabi ga dan Adam. Kamar yadda Bahaushe kan ce, waiwaye adon tafiya, kasar Sin ta shirya bikin tunawa a daidai wannan lokaci, ba don neman ci gaba da kiyayya da juna ba, a maimakon hakan, tana son kira ga al’ummomin duniya da su tsaya tsayin daka a kan kiyaye zaman lafiya da magance yaki a tsakaninsu.

A lokacin kawo karshen bikin faretin da aka yi, tantabaru kimanin dubu 80 ne suka tashi, wadanda suke dauke da sakon fatan alheri na al’ummar Sinawa game da tabbatar da zaman lafiya a duniya. Tabbas kasar Sin za ta nace ga bin hanyar tabbatar da ci gabanta cikin lumana, kuma za ta hada karfi da karfe da al’ummomin duniya, ciki har da na kasashen Afirka, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkanin bil’adama, don ba da gudummawarta wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba na dindindin a fadin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.