ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

A jiya Laraba 3 ga wata, kasar Sin ta gudanar da kasaitaccen bikin faretin soja a birnin Beijing, don tunawa da cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan da ma yakin duniya da tafarkin murdiya, bikin da ya jawo hankalin duniya, har ma wasu abokaina ‘yan Nijeriya sun turo min sakonni, inda suka ce su ma sun kalli gaba dayan bikin, kuma suna mai jinjinawa ga kasar Sin, musamman ganin yadda ta bunkasa har ta zama kasa mai karfin tattalin arziki ta biyu a duniya, bayan yadda ta kasance kasar da aka kai mata hari tare da mamaya a baya. A wata makala da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya wallafa a shafinsa, ya yi nuni da cewa, kwarin gwiwar da jama’ar kasar Sin suka samu daga yaki da maharan kasar Japan ya zama arziki gare su, wanda ya ke matsa musu kaimin tinkarar matsalolin da wahalhalun da ke gabansu, don cimma burin zamanantar da kasarsu da farfado da al’ummun kasar.

Na kuma lura da cewa, shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da shugaban jamhuriyar Congo Denis Sassou Nguesso sun zo kasar Sin don halartar bikin. Kafin ya tashi zuwa kasar Sin, shugaba Sassou ya bayyana cewa, nasarar yakin duniya da tafarkin murdiya ta dogara ne da kokarin da dukkanin al’ummomin duniya masu kishin zaman lafiya da adalci suka yi, idan har masu bin tafarkin murdiya suka cimma nasarar yakin a lokacin, lallai da wuya mu yi zaton irin duhun da dan Adam zai shiga. Ya ce, al’ummar kasar Sin sun bayar da muhimmiyar gudummawa ga cimma nasarar yakin, a yayin da al’ummun kasashen Afirka da dama ma suka sadaukar da rayukansu a yakin, wadanda suka ketare hamadar Sahara da Bahar Rum, suka shiga yakin kafada da kafada tare sojojin kasashen kawance. Abin haka yake, yakin da aka yi da tafarkin murdiya a shekaru 80 da suka wuce, ya kasance turjiyar al’ummomin kasashen duniya, ciki har da na kasar Sin da kasashen Afirka, ga hari da zaluncin mulkin danniya, wanda hakan ya zama nasarar masu kishin adalci da zaman lafiya.

A ganina, dalilin da ya sa bikin tunawa da nasarar da kasar Sin ta shirya ya burge bangarori daban daban na kasashen Afirka, shi ne sabo da abubuwa kusan iri daya ne suka faru a gare su a tarihi, wato dukkansu sun taba fuskantar mamayar mahara da ma mulkin mallaka da aka yi musu, kuma suka samu ‘yancin kansu bisa ga fafatawar da suka yi, har wa yau kuma, dukkansu suna da burin tabbatar da ci gabansu da ma farfado da al’ummunsu. Sakamakon hakan kuma, sun fi fahimta da kishin zaman lafiya da ci gaba.

ADVERTISEMENT

Sai dai ko da yake tuni zaman lafiya da ci gaba sun zama jigon zamanin da muke ciki, amma har yanzu akwai rina a kaba, inda ake ta kara fuskantar matsalolin daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da nuna fin karfi a duniya, kuma zaman lafiya ko yaki, yin shawarwari da juna ko yin fito na fito da juna, cin moriyar juna ko cin nasara daga faduwar wani bangare, ya zama sabon zabi ga dan Adam. Kamar yadda Bahaushe kan ce, waiwaye adon tafiya, kasar Sin ta shirya bikin tunawa a daidai wannan lokaci, ba don neman ci gaba da kiyayya da juna ba, a maimakon hakan, tana son kira ga al’ummomin duniya da su tsaya tsayin daka a kan kiyaye zaman lafiya da magance yaki a tsakaninsu.

A lokacin kawo karshen bikin faretin da aka yi, tantabaru kimanin dubu 80 ne suka tashi, wadanda suke dauke da sakon fatan alheri na al’ummar Sinawa game da tabbatar da zaman lafiya a duniya. Tabbas kasar Sin za ta nace ga bin hanyar tabbatar da ci gabanta cikin lumana, kuma za ta hada karfi da karfe da al’ummomin duniya, ciki har da na kasashen Afirka, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkanin bil’adama, don ba da gudummawarta wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba na dindindin a fadin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

 

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • Sulaiman
    An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.