ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

A jiya Laraba 3 ga wata, kasar Sin ta gudanar da kasaitaccen bikin faretin soja a birnin Beijing, don tunawa da cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan da ma yakin duniya da tafarkin murdiya, bikin da ya jawo hankalin duniya, har ma wasu abokaina ‘yan Nijeriya sun turo min sakonni, inda suka ce su ma sun kalli gaba dayan bikin, kuma suna mai jinjinawa ga kasar Sin, musamman ganin yadda ta bunkasa har ta zama kasa mai karfin tattalin arziki ta biyu a duniya, bayan yadda ta kasance kasar da aka kai mata hari tare da mamaya a baya. A wata makala da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya wallafa a shafinsa, ya yi nuni da cewa, kwarin gwiwar da jama’ar kasar Sin suka samu daga yaki da maharan kasar Japan ya zama arziki gare su, wanda ya ke matsa musu kaimin tinkarar matsalolin da wahalhalun da ke gabansu, don cimma burin zamanantar da kasarsu da farfado da al’ummun kasar.

Na kuma lura da cewa, shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da shugaban jamhuriyar Congo Denis Sassou Nguesso sun zo kasar Sin don halartar bikin. Kafin ya tashi zuwa kasar Sin, shugaba Sassou ya bayyana cewa, nasarar yakin duniya da tafarkin murdiya ta dogara ne da kokarin da dukkanin al’ummomin duniya masu kishin zaman lafiya da adalci suka yi, idan har masu bin tafarkin murdiya suka cimma nasarar yakin a lokacin, lallai da wuya mu yi zaton irin duhun da dan Adam zai shiga. Ya ce, al’ummar kasar Sin sun bayar da muhimmiyar gudummawa ga cimma nasarar yakin, a yayin da al’ummun kasashen Afirka da dama ma suka sadaukar da rayukansu a yakin, wadanda suka ketare hamadar Sahara da Bahar Rum, suka shiga yakin kafada da kafada tare sojojin kasashen kawance. Abin haka yake, yakin da aka yi da tafarkin murdiya a shekaru 80 da suka wuce, ya kasance turjiyar al’ummomin kasashen duniya, ciki har da na kasar Sin da kasashen Afirka, ga hari da zaluncin mulkin danniya, wanda hakan ya zama nasarar masu kishin adalci da zaman lafiya.

A ganina, dalilin da ya sa bikin tunawa da nasarar da kasar Sin ta shirya ya burge bangarori daban daban na kasashen Afirka, shi ne sabo da abubuwa kusan iri daya ne suka faru a gare su a tarihi, wato dukkansu sun taba fuskantar mamayar mahara da ma mulkin mallaka da aka yi musu, kuma suka samu ‘yancin kansu bisa ga fafatawar da suka yi, har wa yau kuma, dukkansu suna da burin tabbatar da ci gabansu da ma farfado da al’ummunsu. Sakamakon hakan kuma, sun fi fahimta da kishin zaman lafiya da ci gaba.

ADVERTISEMENT

Sai dai ko da yake tuni zaman lafiya da ci gaba sun zama jigon zamanin da muke ciki, amma har yanzu akwai rina a kaba, inda ake ta kara fuskantar matsalolin daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da nuna fin karfi a duniya, kuma zaman lafiya ko yaki, yin shawarwari da juna ko yin fito na fito da juna, cin moriyar juna ko cin nasara daga faduwar wani bangare, ya zama sabon zabi ga dan Adam. Kamar yadda Bahaushe kan ce, waiwaye adon tafiya, kasar Sin ta shirya bikin tunawa a daidai wannan lokaci, ba don neman ci gaba da kiyayya da juna ba, a maimakon hakan, tana son kira ga al’ummomin duniya da su tsaya tsayin daka a kan kiyaye zaman lafiya da magance yaki a tsakaninsu.

A lokacin kawo karshen bikin faretin da aka yi, tantabaru kimanin dubu 80 ne suka tashi, wadanda suke dauke da sakon fatan alheri na al’ummar Sinawa game da tabbatar da zaman lafiya a duniya. Tabbas kasar Sin za ta nace ga bin hanyar tabbatar da ci gabanta cikin lumana, kuma za ta hada karfi da karfe da al’ummomin duniya, ciki har da na kasashen Afirka, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkanin bil’adama, don ba da gudummawarta wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba na dindindin a fadin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

 

 

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina
  • Sulaiman
    Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto
  • Sulaiman
    Mutum Ɗaya Ya Mutu, Sama Da 30 Sun Ɓace A Hatsarin Kwale-kwale A Jigawa

MASU ALAKA

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
Ra'ayi Riga

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026
nema

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
Hadarin Kwale-Kwale

Mutum Ɗaya Ya Mutu, Sama Da 30 Sun Ɓace A Hatsarin Kwale-kwale A Jigawa

July 21, 2026
ICPC

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.