• English
  • Business News
Tuesday, September 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

by Sadiq
5 hours ago
in Labarai
0
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ce gwamnatinsa za ta ɗauki nauyin karatun duk wanda ya haddace Alƙur’ani kuma yake son ci gaba da ilimi a fannonin zamani kamar likitanci, ungozoma da sauran sana’o’in zamani.

Ya bayyana haka ne a babban taron da aka gudanar domin gyara tsarin karatun Almajiri da Islamiyya a jihar, inda malamai, shugabannin al’umma, ƙungiyoyi da hukumomi suka halarta.

  • Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
  • Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

Gwamnan ya ce gwamnati za ta kafa sabbin makarantu guda uku da za su haɗa mahaddata Alƙur’ani da ilimin zamani irin su Turanci, Lissafi da koyon sana’o’in hannu ga yara maza da mata.

Makarantar farko za ta kammalu a Katsina kafin ƙarshen nan.

Ya kuma jaddada cewa malamai za su taka muhimmiyar rawa wajen jagorantar wannan shirin, tare da kira ga iyaye da al’umma da su bayar da goyon baya domin gwamnati kaɗai ba za ta iya magance matsalar almajiranci ba.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

Masana da shugabanni da suka halarci taron, ciki har da Farfesa Isah Ali Pantami, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, da sauran fitattun malamai, sun yaba da wannan ƙudiri na gwamnatin Katsina.

Rahotanni sun nuna cewa sama da yara 300,000 ne ba sa zuwa makaranta a Katsina, ciki har da dubban almajirai da ‘yan mata.

Wannan ne ya sa gwamnati ta ɗauki wannan mataki domin inganta ilimi da kuma bai wa matasa damar samun kyakkyawar makoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alƙur’aniDikko RaddaIlimiKatsinaMahaddata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

Related

Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

30 minutes ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

2 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

3 hours ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

6 hours ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

14 hours ago
Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
Labarai

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

16 hours ago
Next Post
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

September 23, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

September 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

September 23, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

September 23, 2025
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

September 23, 2025
He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

September 22, 2025
Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

September 22, 2025
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

September 22, 2025
Nau’o’in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin

Nau’o’in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin

September 22, 2025
Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

September 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.