ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

by Sulaiman
9 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ce Afirka ba ta neman agaji sai dai a haɗin gwiwa na gaskiya bisa girmamawa da adalci.

 

Gwamnan ya kasance babban baƙo mai jawabi a wajen taron baje-kolin kasuwanci tsakanin Kanada da Africa na shekarar 2025, wanda ya gudana a ranar 17 ga Satumba, 2025, a ɗakin otel na Toronto Marriott City da ke Kanada.

ADVERTISEMENT
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas

Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa taron, mai taken “Ƙarfafa Dangantakar Kasuwanci, Zuba Jari da Ci gaba Mai Ɗorewa Tsakanin Kanada da Afrika”, ya haɗa nahiyoyin biyu tare da burin samun ci gaba, ƙirƙire-ƙirƙire, da ɗorewar arziki duk da nisan dake tsakaninsu.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Sanarwar ta ƙara da cewa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa tsarin dimokuraɗiyyar Kanada, ƙarfafan tattalin arziƙi, hakar ma’adinai ta hanyar da ta dace, da kuma harkokin kasuwanci masu zaman kansu masu kirkire-kirkire sun sanya ta zama abokiyar haɗin guiwar da ta ta dace ga Afrika.

 

Ya ce, “Idan Afrika za ta cika burinta gaba ɗaya, dole ne mu gane cewa ci gaba ba wai kawai batun manufofin ƙasa bane; yana kuma buƙatar aikace-aikacen matakan jihohi da ƙananan hukumomi.

 

“Yayin da Gwamnatocin Tarayya ke ba da jagorar manufofi, a matakin Jihohi, larduna, da Ƙananan Hukumomi ake fassara alƙawuran kasuwanci, zuba jari da ci gaba zuwa ainihin gaskiya.

 

“Matakan jihohi sune inda manoma ke noma abincin da ke ciyar da ƙasashe, inda aikin haƙar ma’adinai ke yin nasara ko faɗuwa, inda matasa ke neman dama, da inda masu zuba jari ke bukatar tsari mai bayyana, kwanciyar hankali, da dawowa mai adalci. Wannan shi ya sa kasancewata a nan a matsayin Gwamnan Zamfara ba da gangan bane, illa da nufin ƙarfafawa. Yana nuna cewa tashin hankali na Afrika zai samo asali ne daga jihohi da larduna kamar yadda zai fito daga manyan birane.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na canza tsarin mulki a Zamfara da yanayin saka jari don jawo hankalin abokan hulɗa masu gaskiya waɗanda ke da darajar gaskiya, rikon amana, da ci gaba mai ɗorewa.

 

“Noma shi ne ginshiƙin tattalin arziƙinmu. Fiye da kashi 70 na ƙasar mu tana da filin noma, Zamfara na iya zama amfanin gona ga Nijeriya da ma nahiyar Afrika. Muna neman haɗin kai a fannonin injina, ban ruwa, kula da amfanin gona bayan girbi, ajiya, da sarrafa kayan gona. Kwarewar Kanada, haɗe da jajircewar manomanmu, na iya samar da sabon tsarin tsaron abinci ga Afrika.

 

“Baya ga noma, Zamfara na da ma’adinai masu daraja kamar zinariya, lithium, manganese, da granite waɗanda suke da muhimmanci ga sauyin makamashi. Muna ƙoƙarin koyon darasi daga kurakurai na baya, domin tabbatar da cewa arzikin albarkatu ya fassaru zuwa ci gaba, ba wai fitarwa kawai ba. Muna ƙarfafa dokoki, inganta hakar ma’adinai na gaskiya, da tabbatar da amfanin al’umma.”

 

“Ina kira ga abokanmu na Kanada da su duba bayan manyan biranen Afrika zuwa yankuna, gonaki, makarantun, masana’antu, da al’ummomi, inda ainihin haɗin kai zai bunƙasa. Ku ƙarfafa shugabannin Afrika, ciki har da ni, wajen yin garambawul, ƙarfafa mulki, tsayawa kan gaskiya, da gina muhalli mai kyau ga haɗin kai.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Nau’o’in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin

Nau'o'in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.