• English
  • Business News
Thursday, September 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

by Abubakar Sulaiman
6 hours ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ambaliyar ruwa ta mamaye a ƙalla unguwanni tara a ƙananan hukumomin Ibaji da Kogi, inda ta lalata gonaki da gidaje tare da raba dubban jama’a da muhallansu. Sakataren hukumar agajin gaggawa ta jihar (SEMA), Mukhtar Atima, ya bayyana hakan a Lokoja, inda ya ce an buɗe sansanonin rikon ƙwarya 42 domin sauƙaƙa wa waɗanda abin ya shafa.

Rahotanni sun nuna cewa a shekarar 2024, ambaliya ta tilasta wa mutane sama da miliyan biyu barin gidajensu a ƙananan hukumomi tara na jihar. Wannan ya jawo lalacewar makarantu, da asibitoci, da hanyoyi, da gadoji, da kuma lalata gonaki, inda manoma musamman masu noman doya suka fi fuskantar asara mai girma. Wasu daga cikinsu sun yi gaggawar girbi kafin lokacin da ya dace don guje wa asarar jarinsu, musamman waɗanda suka karɓi bashi daga bankuna.

  • Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa
  • Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

A wasu sassan jihar, ambaliya ta katse manyan hanyoyin shiga da fita, lamarin da ya ƙara tsananta wahalar kai ɗauki. Shugaban ƙungiyar ci gaban Kupa (KUDA), Sa’idu Bn Malik, ya ce ambaliyar ta durƙusar da tattalin arziƙin yankin, ta lalata hanyoyin mota, kuma ta ƙara jefa al’umma cikin barazanar kamuwa da rashin lafiya da jawo rashin tsaro.

A jihar Legas kuwa, ruwan sama mai yawa ya rufe muhimman unguwanni ciki har da Lekki, da Mile 2, da 3rd Mainland Bridge, da Ago Palace. Jama’a sun koka da toshewar magudanan ruwa da kuma rashin gaggawar gwamnatin jihar wajen bada agaji.

Daily Trust ta rawaito cewa, Mazauna yankunan sun ce harkokin sufuri sun tsaya cak, gidaje da kadarori sun lalace, yayin da aka tilasta wa wasu barin motoci su yi tafiya a ƙafa. Wasu kuma sun bayyana yadda aikin gina hanya a Lekki ya kara tsananta cunkoso da halin da ake ciki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmbaliyaFloodKogiLagosLegasRuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Next Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Related

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

2 hours ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

2 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

5 hours ago
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki
Manyan Labarai

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

9 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

LABARAI MASU NASABA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

September 25, 2025
Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

September 25, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

September 25, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

September 25, 2025
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

September 25, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

September 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

September 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

September 25, 2025
Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.