• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

by Idris Aliyu Daudawa
4 hours ago
in Rahotonni
0
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawancin wadanda suka kammala jami’oi a Nijeriya suna yin wasu kananan ayyuka ko sana’oi wadanda idan da ace akwai ayyukan yi wadanda suka fi su ba za su taba yin su ba, musamman ma idan aka yi la’akari da wahalhalun da suka fuskanta kafin su kai ga kammala karatu, hakan shi yasa suka hira da wakilan jaridar LEADERSHIP inda suka yi bayanai na yadda suke fuskanta matsin rayuwa :sun bayyana dalilan da suka sa suke yin ayyukan; me ya kai ga har, sa su yanke shawarar yin hakan, wace irin dadewa suka yi suna tafiyar da ayyukan, da kuma irin yadda muatne suke kallonsu saboda aikin nasu.

EBONYI: A Jihar Ebonyi wadanda suka kammala jami’oi suna aiki ne Hotel inda suke aikin bada barasa wato giya, ‘yan Okada, da kuma masu tuka Keke Napep.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A, Abakaliki hedikwatar Jihar Ebonyi da wasu garuruwa na kewaye da ita an lura da cewa yawancin wadanda suka kammala jami’oin sun samu kansu ne cikin kananan ayyuka wadanda idan ba domin rayuwa ce ta canza ba, kuma samun aikin yana da wuya, hakan ce ta sa su, kamar wadanda suna aiki a Hotel domin kai Barasa ga wadanda suke bukata, masu kula da wuraren ajiye kaya, Okada, da kuma yaron mota wanda zai rika yi, A hirar da suka yi da LEADERSHIP ta Lahadi sun bayyana cewa sun yanke shawarar da su yi ire- iren ayyukan ne saboda ko ba komai za su samu abubuwan da za su rika cin abinci, su kula da kannensu, da kuma Iyaye, bugu da kari kuma, domin su kaucewa irin tunanin nan da zai sasu, aikata laifukan da basu da kyau kamar, Karuwanci, da kuma sauran ayyukan da basu dace ba ace ana aikata su.

Mace da ta kammala jami’a ta karanta lamarin daya shafi aikin Jarida a Jami’ar Jihar Ebonyi (EBSU) , Miss Ifeanyinwa Oforbiike, wadda ita ma tana aiki ne a Hotel a matsayin mai raba Barasa a wani katafaren Otel Abakaliki, tace ana biyanta alabashin Naira30, 000 kowane wata ta yi dana-sani domin kuwa kamar yadda tayi bayani aka share wata uku zuwa hudu, kafin abiyata albashin wata daya a matsayin daga cikin bashin da take bi.

Tace bayan kammala karatunta ta nemi aiyukan yi daban- daban, ta bangaren hukumomin gwamnati da kuma na masu zaman kansu, sai dai kash! ba ta, samu nasara ba kamar yadda ta jaddada.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

“Daga baya kuma sai ta fada cikin lamarin yin Takalma, sai dai abin ban takaici, ba tada isassun kudaden da za su taimaka mata don sabuwar harkar yin Takalma sana’ar da tasa kanta. Tana fatan idan ta samu isassun kudade, za ta sake komawa harkar.”

Miss Oforbiike ta kara yin bayanin ta hadu da abubuwan takaici, an maida ta wata ba kome ba, sai bakaken maganganu da ta fuskanta lokacin da take tafiyar da harkar.

Mista Celab Ogodo ya ce ‘Ina samun kudade da yawa ta hanyar tuka KekeNapep fiye da ma’aikatan gwamnati’

Ya kammmala karatunsa ne daga Kwalejin ilimi ta Jihar Ebonyi, ya ce shi bai dauki aikinsa kamar wanda bai dace ba, domin kullum yana samun Naira 15,000 bayan wasu kudaden da ya kashe.

AKWA IBOM: Wadanda suka kammala jami’a suna aiki kamar, Direbobin motar daukar fasinja, da kuma saayar da Kifi

Duk da Jihar tana daga cikin Jihohin da suke samar da Manfetur a Kudu maso Kudu, wadanda suka kammala Jami’oi suna tafiyar da rayuwarsu ta kudaden da suka samu ta hanyar kananan ayyukan da basu samun kudaden da za su ishe su tafiyar da rayuwa, irinsu suna da yawa a Jihar ta Akwa Ibom, musamman ma zirga – zirga, bangaren shari’a, sana’ar da bata taka kara ta karya ba a harkar ruwa, a wuraren da suke kusa da ruwa.

Wasu daga cikinsu,wadanda suke harkokin zurga- zurga domin samun abin rufawa kai asiri, sun bayyana wahalhalun da suka sha, bayan kammala karatun jami’a fiye da shekara 10 “amma babu wani ci gaban da ak samu.”

Ekene Stephen, shi ya karanta Philosophy ne kamar yadda ya ce: “Na kammala Jami’ar UYO tun shekarar 2011, amma har yanzu ban samu wani aiki mai nagarta ba.Na yi kokarin samun aikin gwamnati matsayin Malamin makaranta, amma har yanzu ban samu ba. An dauke ni aikin Malamin makaranta mai zaman kanta a God’s Power International School, amma albashi Naira 35,000 ne suke bani.

 

BENUWE:

A Jihar Benuwe, wasu daga cikin wadanda suka kammala Jami’a suna tuka Okada ne da kuma sayar da ruwan fiyo water da snack, domin kawai su samu damar na abinci da sauaran wasu abubuwa.

A tattaunawar da aka yi da shi, Ijiir-Iter Thomas, da ya kammala karatu, ya kuma karanta Geography daga Jami’ar Jihar Benuwe, 2007 ya ce tun da ya gama aikin yiwa kasa hidima (NYSC), ya nemi bukatar daukje shi ayyuka daban daban ciki da wajen Jihar, amma bai samu sa’ar samu ba, don haka ya yanke shawarar ya fara, da sayar da snacks (shawarma) a bakin titi, sana’ar daya koya a sansanin masu yiwa kasa hidima.

 

Kamar yadda ya ce da farko, naji tsoron irin maganganun da mutane za su yi – Dan Okada

 

RIBAS: Wadanda suka kammala Jami’a suna sana’ar sayar da manfetur a gidajen mai da kuma Malamai a makarantu masu zaman kansu.

Yawancin wadanda suka kammala Jami’a a Jihar Ribas suna yin wasu ayyukan da wasu kudade ake samu masu yaw aba, abinda ya fara daga msu sayar da man fetur a gidajen mai, da kuma kasancewa masu gadi, wadanda za su rika canjin iki saboda su rika zuwa aiki a makarantu masu zaman kansu.

Da take hira da Jaridar LEADERSHIP ta karshen mako, Ifeoma Cletus, da ta karanta Philosophy, tana koyarwa ne a wata makaranta mai zaman kanta a Fatakwal, tace rashin samun aikin ya sa ta yanke shawarar aikin koyarwa.

 

KADUNA:

A jihar Kaduna wasu daga cikin wadanda suka kammala Jami’a wadanda suka zanta da LEADERSHIP ta krshen mako sun bayyana rashin ingantattun ayyuka, da kuma irin matsin tattalin arzikin d ake fuskanta yanzu, na daga cikin manyan dalilan da suka sa su shiga irin su ayyukan da suke yi, domin kawai su samu damar tafiya da rayuwa, Wadanda suka kammala jami’a suna yin aiki ne a matsayin masu shara da goge a Otel ko kuma sana’ar Okada.

Mark Bala ya karanta Turanci ne a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, shi ma shi yake tukawa domin ya rufawa kan sa asiri abinda aka fi sani da Okada Rider, cewa ya kwashe shekara shida yana neman aiki amma bai samu ba.

Ya ce “Bayan ya kammala yiwa kasa hidima, a shekarar 2019, Ina nemi ayyukan yi, daga gwamanti da kuma wurare masu zaman kansu ba tare da ya samu ba. Ni yanzu mai sana’ar Okada ne.Ina ci da kaina da kuma iyalina, a a halin yanzu wannan shi ne aiki na. Wani lokaci na kan koma gida da Naira ku san 10,000 kowace rana bayan idan akwai gyare- gyare da kuma sayen mai.”

 

DELTA: Wadanda suka kammala jami’a suna aikin gyran mota, masu hana hatsaniya a gidajen shakatawa (Otel) da kuma kashe Beraye

Lokacin da Kareem Usman ya iso, birnin Benin, a shekarar 2015 bayan ya kammala yiwa kasa hidima, ya yi tsammanin ai shi zai samu kwanciyar hankali. Bayan shekarun da yayi na karade Nijeriyta wajen neman aiki, aiki da Kamfanin tayis na Chaina a gundumar Utesi a lokacin yana yiu ma kan sa kallon babu wanda ya fi shi sa’a.

“Ya zo birnin Benin ne saboda yayi aiki da Kamfanin Chaina wanda yake yi tayis,” ya tuna da wata ganawar da aka yi ma shi. “Kamfanin yana gundumar Utesi ne.”

Amma kuma daga baya sai farincikin da yake da shi ya koma bakin ciki.

“Saboda albshin bai taka kara ya karya bane ba zai ishe shi yin wani abu ba,” kamar yadda ya bayyana.“Ya yi shekara biyar kafin ya bar wurin. Saboda wurin da ya yi aiki idan ya yi kwana biyar bai je aiki ba, shikenan ya rasa albashin watan ke nan.”

 

ANAMBRA: Wadanda suka kammala jami’a suna aikin direbobin motocin fasinja da masu lura cunkoson abubuwan hawa

Chidiebere Chibueze, mai shekara 31, da Chioma Ifediorah suna daga cikin wadanda suka kammal akaratun Jami’a masu yawa a Awka, Jihar Anambra , wadanda dole ce ta sa, su ayyukan da suke yiu yanzu domin neman su tsira da mutuncinsu.

Yayin da Chibueze ya yi karatuns a a Jami’ar Jihar Imo 2015 da digirin din lamarin kasuwanci, Chioma ita kuma ta kammala Jami’ar Azikiwe Unibersity (UNIZIK), a Awka, shekarar 2009 da digiri din yadda za’a tafiyar da harkokin kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

Next Post

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Related

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 hour ago
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC
Rahotonni

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

18 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

1 week ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 weeks ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 weeks ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

3 weeks ago
Next Post
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

LABARAI MASU NASABA

Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

September 27, 2025
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

September 27, 2025
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

September 27, 2025
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

September 27, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

September 27, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.