ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

by Sani Anwar
8 months ago
Siyasa

Yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, jam’iyyun siyasa Nijeriya na dakon jiran ganin sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wanda suka kara jaddada muhimmancin samun sahihin zabe da rashin son zuciya da sadaukarwa ga ka’idojin dimokuradiyya.

A cikin wata tattaunawa ta musamman da manema labarai, APC ta bukaci sabon shugaban INEC da ya tabbatar da cewa kowacce jam’iyyar siyasa ta samu martaba daidai ga dukkan jam’iyyun Nijeriya, yayin da PDP ta jaddada bukatar shugaban hukumar ya kasance mai zaman kansa da kuma cin gashin kansa.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

A gefe guda kuma, ADC ta gargadi cewa rashin gudanar da zabe mai inganci a karkashin sabon shugaban INEC na iya zama barazana ga zaman lafiyar dimokuradiyya a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Shugaban INEC na yanzu, Farfesa Mahmood Yakubu, yana shirin kammala wa’adinsa na biyu kafin watan Nuwamba.

An nada shi a 2015, kuma an sake kara masa wa’adi na biyu a 2020, Yakubu yana da daya daga cikin shugabanin INEC da suka fi dadewa a tarihin hukumar zaben Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Bisa sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ” shugaban kasa ne zai nada shugaban INEC da mambobin hukumar zabe ta kasa, sannan majalisar dattawa ta tabbatar da su.”

Dangane da tanadin da ke cikin tsarin mulki, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya tanadi jerin sunayen ‘yan takara da za su meye gurbin Yakubu.

Da yake jawabi kan tsammanin jam’iyyar APC mai mulki, daraktan yada labarai, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa yayin da jam’iyyar ke nufin lashe duk zabe, tana jaddada bukatar samun yin aldaci ga kowa.

Ibrahim, a cikin wata hira, ya bayyana cewa, “A matsayinmu na jam’iyya, abin da muka sa a gaba shi ne samun nasarar cin zabe mai cike da inganci.”

“Babban burinmu shi ne, yadda za mu karbe iko ta hanyar da za ta ba da riba ga dimokuradiyya ga mutane. burinmu ita ce yadda za mu tsaya takara a zabe kuma a ba mu damar taka ba tare da an dakatar da mu ko an cire mu daga zabe ba.

“Don haka, muna sa ran samun shugaban hukumar zabe wanda zai ba da dama ga kowa, wanda zai ba da damar gudanar da zabe cikin ‘yanci da adalci. Muna bukatar shugaban INEC da zai yi aiki ka doka.”

Sakataren yada labarai jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba, ya jaddada cewa dole ne shugaban INEC da zai zo ya zama mutum mai nagarta.

Ologunagba ya kuma kira ga shugaban kasa da masu ruwa da tsaki masu alkakkin zaben shugaban INEC su yi la’akari da halayen ‘yan takarar sosai kuma su tabbatar an nada mutumin da ke da kwarewa.

Ya bayyana cewa, “Shugaban INEC na gaba ya zama wani mutum mai nagarta, ya zama wanda ba zai kasance mai mummunan hali ba, ya zama mai adalci, wanda zai zama mai ‘yanci kuma ya gudanar da hukumar ta wannan hanyar, kamar yadda doka ta tanada. Don haka wannan shi ne abin da muke tsammani.”

Ita kuwa jam’iyyar hadaka, ta bakin sakataren yada labarai na kasa, Bolaji Abdulahi, ta bayyana damuwa kan rikicin bai wa INEC ‘yancin kanta.

Abdullahi ya bayyana cewa sabon shugaban INEC da za a zaba dole ne ya yi aiki don dawo da amincewa ta hanyar tabbatar da gudanar da zabe mai inganci a 2027.

Ya ce, “Abu mafi muhimmanci shi ne, ina tunanin INEC ta sha fama da rikice-rikice na samun amincewa a idon masu kada kuri’a a Nijeriya a cikin shekaru da dama.”

“Sabon shugaban INEC ya kamata ya tabbatar da cewa hukumar ta ci gaba da kasancewa a matakin amincewa. Ka san cewa, tabbatar da tsarin zabe yana karfafa gwiwar kowa, kuma shi ne kawai hanyar da za a tabbatar da kwanciyar hankali a cikin kasar nan.

“Dole ne su tabbatar da nada mtumin da zai kasance tsayayye da kuma jajircewa. Idan aka kasa yin hakan, hakan na iya haifar da shakku a cikin zukatan ‘yan kasa game da ingancin zaben 2027, ko za su kasance masu ‘yanci da adalci kan zaben.

“Don haka, ina tsammanin shekara ta 2027 za ta zama mai muhimmanci ga kowa. A matsayin jam’iyya, muna fatan cewa nadin zai ba da damar ga wanda ya fahimci muhimmancin tarihi na aikin.”

Siyasa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Siyasa
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Siyasa
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.