• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
18 hours ago
Idanu

Wani matashi mai suna Auwalu Muhammad ya kwaƙule idanuwan ƙannuwarsa ‘yar shekara bakwai a duniya, Rukayya Muhammad, domin yin tsafin neman kuɗi a yunƙurinsa na zama hamshaƙin mai kuɗi. 

Wannan dai na zuwa ne bayan da Boka mai bayar da sa’ar yin kuɗi da ke sanya jama’a ciro sassan jikin mutane kamar idanu da azzakari ya nemi Auwalu da ya ciro idanun yarinyar domin a masa tsafi ya zama mai kuɗi dare guda. 

  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi
  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi

A halin yanzu likita ya tabbatar da cewar Rukayya ba za ta sake gani ba domin idanuwanta sun lalace gaba ɗaya. 

Wannan abun takaici ya faru ne a yankin Wailo da ke ƙaramar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi.

A lokacin da ake zantawa da mahaifin yarinyar ya bayyana cewar wanda ake zargin (Auwalu) ya yaudari ‘yar uwar tasa, wacce suke da iyaye guda tare, zuwa daji tare da kwaƙule mata idanu da ƙarfin tsiya. 

LABARAI MASU NASABA

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Mahaifin Rukayya, Muhammad Adamu mazaunin ƙauyen Bayan Dutse da ke Wailo, a gundumar Kubi cikin ƙaramar hukumar Ganjuwa a ranar 17 ga watan Oktoba ya kai rahoton caji ofis ɗin Soro ya ke shaida cewar wani matashi mai suna Auwal Dahiru mai shekara 17, ya kai farmaƙi wa yarsa da ƙoƙarin kasheta da kwaƙule mata idanuwanta. 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil a ranar Litinin, ya ce, lokacin da ‘yansanda suka samu rahoton faruwar lamarin cikin gaggawa a ƙarƙashin Baturen ɗansanda da ke kula da caji ofis ɗin Soro, CSP Aliyu Mohammad Goni, sun kai agaji inda lamarin ya faru.

A lokacin da aka ɗauki Rukayya zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, domin mata jinya, kwararren likitan Ido a asibitin ya tabbatar da cewar yarinyar ba za ta sake gani da idanuwanta ba har ƙarshen rayuwarta. 

Kan haka ne rundunar ‘yansandan ta ce zuwa yanzu ta cafke mutane shida da ake zargi da hannu kan wannan aika-aikar waɗanda suka haɗa da Auwal Dahiru, mai shekara 17 da ke Bayan Dutse, Wailo, Kubi, Ganjuwa, Mohammed Rabiu (mai shekaru 19), Saleh Ibrahim (20), Nasiru Muhammad mazaunin cikin garin Soro a Ganjuwa, Hassan Garba mazaunin Soro da kuma Garba Dahiru mai shekara 43 a duniya kuma mazaunin Soro.

“Lokacin da ake bincike, waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu,” Wakil ya tabbatar.

Jami’in watsa labaran ‘yansandan ya kuma sanar da cewa yanzu haka bincike na ci gaba da gudana domin zaƙulo dukkanin masu hannu a wannan aikin domin su fuskanci Shari’a. 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi,  State Command, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci a gaggauta maida binciken kes ɗin zuwa sashin binciken manyan laifukan (SCID), Bauchi domin faɗaɗa bincike da gano wasu abubuwan da suke akwai kan lamarin. 

Ya bayar da tabbacin wanzar da gaskiya da adalci kan lamarin da yin aiki bisa kwarewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)
Manyan Labarai

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Next Post
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.