• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zauren Al’ummar Hausawa Ta Duniya Ta Nada Sarkin Zazzau Uban Kungiya

by Bello Hamza
3 years ago
in Labarai
0
Kungiyar Zauren Al’ummar Hausawa Ta Duniya Ta Nada Sarkin Zazzau Uban Kungiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne kuniyar zauren al’ummar Hausawan Duniya, cikin bukuwan ranar Hausawan Duniya ta kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ziyara, tare da zabarsa a matsayin uban wannan kungiya.

Cikin jawabinsa na maraba, Mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ya nuna godiyarsa ga Allah ya ba da ikon kabar bakuncin wadannan baki nasa.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Mai Martaba Sarki ya ce, “muna mika matukar godiyar mu ga Allah da ya ba mu ikon ganin wannan rana cikin koshin lafiya har muka karbi bakuncin ku.

Muna godiya ga Allah da ya kawo ku lafiya, tate da fatan za ku koma lafiya.”

Haka kuma Sarkin ya nuna farin cikinsa da zabarsa da aka yi a matsayin Uba na wannan kungiya ta Zauren al’ummar Hausawan Duniya, “ba abin da za mu ce sai dai Allah saka maku da alhairi,” in ji Sarki.

Labarai Masu Nasaba

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Ya ci gaba da bayyana cewa saboda muhimmancin wannan rana da kuma al’ummar Hausan Duniya, “ya zama wajibi a gare mu mu karbi wannan girma da aka dora mana.

Tare da fatan Allah zai mana ludufi ya ba mu ikon dauka,” In ji Sarkin na Zazzau.

Cikin zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan kammala wannan ziyara, Shugaban zauren Hausa ta duniya, Ambasada Muhammad Kabir Gure ya bayyana cewa sun zabi kawo wannan ziyara a wannan rana ce domin muhimmancin ranar, wacce ya ce Majalisar Dinkin Duniya ta ware don Hausan duniya.

“Wannan muhimmiyar rana ce a gare mu, shi ne muka kawo wa Mai martaba Sarkin Zazzau ziyara domin ya sanya mana albarka.

Kuma a matsayinsa na Uba, ya sa mu ka zo neman albarka, wanda kuma a yanzu haka mun ba shi matsayin Uba na wannan kungiya,” in ji Ambasada.

Alhaji Sanusi ya kara da cewa a halin da ake ciki, Bahaushe bai isa ya tashi ya yi doguwar tafiya cikin kwanciyar hankali ba, “saboda haka sai muka ga ashe ke nan ba biki ya kamata mu yi ba, alhini za mu nuna, ai ranar bikinmu, ita ce ranar da ‘yan uwanmu suka fito daga daji,” in ji shi.

Ya ce, wannan ne ya sa suka zo wurin mai martaba Sarkin Zazzau domin jajanta wa juna, tare da yin kira ga gwamnati ta hanzarta karbo mutanenmu da ke dazuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmed Nuhu BamalliMai MartabaNadiSarautaSarkiSarkin Zazzau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Manoman Shinkafa Ke Fuskanta A Kano

Next Post

Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al’Æ™ur’ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

Related

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

23 minutes ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

3 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

5 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

7 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

18 hours ago
Next Post
Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al’Æ™ur’ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al'ƙur'ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.