ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zauren Al’ummar Hausawa Ta Duniya Ta Nada Sarkin Zazzau Uban Kungiya

by Bello Hamza
4 years ago
Hausawa

A kwanakin baya ne kuniyar zauren al’ummar Hausawan Duniya, cikin bukuwan ranar Hausawan Duniya ta kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ziyara, tare da zabarsa a matsayin uban wannan kungiya.

Cikin jawabinsa na maraba, Mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ya nuna godiyarsa ga Allah ya ba da ikon kabar bakuncin wadannan baki nasa.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Mai Martaba Sarki ya ce, “muna mika matukar godiyar mu ga Allah da ya ba mu ikon ganin wannan rana cikin koshin lafiya har muka karbi bakuncin ku.

ADVERTISEMENT

Muna godiya ga Allah da ya kawo ku lafiya, tate da fatan za ku koma lafiya.”

Haka kuma Sarkin ya nuna farin cikinsa da zabarsa da aka yi a matsayin Uba na wannan kungiya ta Zauren al’ummar Hausawan Duniya, “ba abin da za mu ce sai dai Allah saka maku da alhairi,” in ji Sarki.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ci gaba da bayyana cewa saboda muhimmancin wannan rana da kuma al’ummar Hausan Duniya, “ya zama wajibi a gare mu mu karbi wannan girma da aka dora mana.

Tare da fatan Allah zai mana ludufi ya ba mu ikon dauka,” In ji Sarkin na Zazzau.

Cikin zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan kammala wannan ziyara, Shugaban zauren Hausa ta duniya, Ambasada Muhammad Kabir Gure ya bayyana cewa sun zabi kawo wannan ziyara a wannan rana ce domin muhimmancin ranar, wacce ya ce Majalisar Dinkin Duniya ta ware don Hausan duniya.

“Wannan muhimmiyar rana ce a gare mu, shi ne muka kawo wa Mai martaba Sarkin Zazzau ziyara domin ya sanya mana albarka.

Kuma a matsayinsa na Uba, ya sa mu ka zo neman albarka, wanda kuma a yanzu haka mun ba shi matsayin Uba na wannan kungiya,” in ji Ambasada.

Alhaji Sanusi ya kara da cewa a halin da ake ciki, Bahaushe bai isa ya tashi ya yi doguwar tafiya cikin kwanciyar hankali ba, “saboda haka sai muka ga ashe ke nan ba biki ya kamata mu yi ba, alhini za mu nuna, ai ranar bikinmu, ita ce ranar da ‘yan uwanmu suka fito daga daji,” in ji shi.

Ya ce, wannan ne ya sa suka zo wurin mai martaba Sarkin Zazzau domin jajanta wa juna, tare da yin kira ga gwamnati ta hanzarta karbo mutanenmu da ke dazuka.

Hausawa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al’ƙur’ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al'ƙur'ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.