ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Ɗage Taronta Bayan Arangamar ‘Yansanda Da ‘Yan Daba A Abuja

by Sadiq
1 month ago
PDP

A ranar Talata, an samu tashin hankali a shalkwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja bayan ‘yan daba daga ɓangarori biyu da ke taƙaddama da juna sun yi artabu a ofishin jam’iyyar.

Rigimar ta fara ne da sassafe lokacin da magoya bayan dakataccen sakataren jam’iyyar, Sanata Samuel Anyanwu, suka iso wajen da misalin ƙarfe 8 na safe.

  • Zaɓen 2027: Malami Zai Fito Takarar Gwamna A  Kebbi
  • ’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

Sun ce sun isa ofishin ne domin karɓar ragamar jam’iyyar bayan gudanar da taron jam’iyyar a makon da ya gabata.

ADVERTISEMENT

Amma magoya bayan shugaban jam’iyyar na riƙon kwarya, Ambasada Umar Damagum, suka taru domin hana su shiga.

Lamarin ya yi ƙamari, inda ‘yan daba daga ɓangarorin biyu suka afka wa juna da faɗa.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

’Yansanda da ke wajen sun yi ƙoƙarin kwantar da tarzomar, duk da cewa manyan jam’iyyar kamar Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, suna wajen.

Daga ƙarshe, ’yansanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa su.

Wannan ya sa ’yan jarida, ma’aikata da mambobin jam’iyyar suka nemi mafaka, yayin da wasu mutane suka ji rauni.

Rikicin ya yi sanadin lalata wasu kadarorin hedikwatar jam’iyyar.

Saboda wannan tashin hankali, sabon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya sanar da ɗage taron farko na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) da aka shirya yi a ranar Talatar.

Da yake magana da ’yan jarida, Turaki ya ce an ɗage taron zuwa ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.

Ya zargi “maƙiyan ci gaba da maƙiyan dimokuraɗiyya” da haddasa rikicin.

Turaki, ya gode wa Kwamishinan ’Yansandan Abuja, saboda samar da tsaro.

Ya kuma yaba wa gwamnoni, ’yan majalisa, tsofaffin ministoci, shugabannin jam’iyya da sauran manyan jam’iyyar saboda goyon bayansu.

Ya ce PDP jam’iyya ce mai son zaman lafiya, kuma dole ta ci gaba da kasancewa a haka domin samun damar kowawa mulki.

Rikicin shugabanci ya ƙara tsananta bayan da jam’iyyar ta kori Samuel Anyanwu, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wasu da ake zargi da cin amanar jam’iyyar.

Magoya bayansu su ma sun shirya yin nasu taron a hedikwatar jam’iyyar a ranar Talata, lamarin da ya ƙara dagula al’amura.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.