ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Ɗage Taronta Bayan Arangamar ‘Yansanda Da ‘Yan Daba A Abuja

by Sadiq
8 months ago
PDP

A ranar Talata, an samu tashin hankali a shalkwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja bayan ‘yan daba daga ɓangarori biyu da ke taƙaddama da juna sun yi artabu a ofishin jam’iyyar.

Rigimar ta fara ne da sassafe lokacin da magoya bayan dakataccen sakataren jam’iyyar, Sanata Samuel Anyanwu, suka iso wajen da misalin ƙarfe 8 na safe.

  • Zaɓen 2027: Malami Zai Fito Takarar Gwamna A  Kebbi
  • ’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

Sun ce sun isa ofishin ne domin karɓar ragamar jam’iyyar bayan gudanar da taron jam’iyyar a makon da ya gabata.

ADVERTISEMENT

Amma magoya bayan shugaban jam’iyyar na riƙon kwarya, Ambasada Umar Damagum, suka taru domin hana su shiga.

Lamarin ya yi ƙamari, inda ‘yan daba daga ɓangarorin biyu suka afka wa juna da faɗa.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

’Yansanda da ke wajen sun yi ƙoƙarin kwantar da tarzomar, duk da cewa manyan jam’iyyar kamar Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, suna wajen.

Daga ƙarshe, ’yansanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa su.

Wannan ya sa ’yan jarida, ma’aikata da mambobin jam’iyyar suka nemi mafaka, yayin da wasu mutane suka ji rauni.

Rikicin ya yi sanadin lalata wasu kadarorin hedikwatar jam’iyyar.

Saboda wannan tashin hankali, sabon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya sanar da ɗage taron farko na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) da aka shirya yi a ranar Talatar.

Da yake magana da ’yan jarida, Turaki ya ce an ɗage taron zuwa ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.

Ya zargi “maƙiyan ci gaba da maƙiyan dimokuraɗiyya” da haddasa rikicin.

Turaki, ya gode wa Kwamishinan ’Yansandan Abuja, saboda samar da tsaro.

Ya kuma yaba wa gwamnoni, ’yan majalisa, tsofaffin ministoci, shugabannin jam’iyya da sauran manyan jam’iyyar saboda goyon bayansu.

Ya ce PDP jam’iyya ce mai son zaman lafiya, kuma dole ta ci gaba da kasancewa a haka domin samun damar kowawa mulki.

Rikicin shugabanci ya ƙara tsananta bayan da jam’iyyar ta kori Samuel Anyanwu, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wasu da ake zargi da cin amanar jam’iyyar.

Magoya bayansu su ma sun shirya yin nasu taron a hedikwatar jam’iyyar a ranar Talata, lamarin da ya ƙara dagula al’amura.

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.