ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Ɗage Taronta Bayan Arangamar ‘Yansanda Da ‘Yan Daba A Abuja

by Sadiq
8 months ago
PDP

A ranar Talata, an samu tashin hankali a shalkwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja bayan ‘yan daba daga ɓangarori biyu da ke taƙaddama da juna sun yi artabu a ofishin jam’iyyar.

Rigimar ta fara ne da sassafe lokacin da magoya bayan dakataccen sakataren jam’iyyar, Sanata Samuel Anyanwu, suka iso wajen da misalin ƙarfe 8 na safe.

  • Zaɓen 2027: Malami Zai Fito Takarar Gwamna A  Kebbi
  • ’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

Sun ce sun isa ofishin ne domin karɓar ragamar jam’iyyar bayan gudanar da taron jam’iyyar a makon da ya gabata.

ADVERTISEMENT

Amma magoya bayan shugaban jam’iyyar na riƙon kwarya, Ambasada Umar Damagum, suka taru domin hana su shiga.

Lamarin ya yi ƙamari, inda ‘yan daba daga ɓangarorin biyu suka afka wa juna da faɗa.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

’Yansanda da ke wajen sun yi ƙoƙarin kwantar da tarzomar, duk da cewa manyan jam’iyyar kamar Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, suna wajen.

Daga ƙarshe, ’yansanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa su.

Wannan ya sa ’yan jarida, ma’aikata da mambobin jam’iyyar suka nemi mafaka, yayin da wasu mutane suka ji rauni.

Rikicin ya yi sanadin lalata wasu kadarorin hedikwatar jam’iyyar.

Saboda wannan tashin hankali, sabon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya sanar da ɗage taron farko na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) da aka shirya yi a ranar Talatar.

Da yake magana da ’yan jarida, Turaki ya ce an ɗage taron zuwa ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.

Ya zargi “maƙiyan ci gaba da maƙiyan dimokuraɗiyya” da haddasa rikicin.

Turaki, ya gode wa Kwamishinan ’Yansandan Abuja, saboda samar da tsaro.

Ya kuma yaba wa gwamnoni, ’yan majalisa, tsofaffin ministoci, shugabannin jam’iyya da sauran manyan jam’iyyar saboda goyon bayansu.

Ya ce PDP jam’iyya ce mai son zaman lafiya, kuma dole ta ci gaba da kasancewa a haka domin samun damar kowawa mulki.

Rikicin shugabanci ya ƙara tsananta bayan da jam’iyyar ta kori Samuel Anyanwu, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wasu da ake zargi da cin amanar jam’iyyar.

Magoya bayansu su ma sun shirya yin nasu taron a hedikwatar jam’iyyar a ranar Talata, lamarin da ya ƙara dagula al’amura.

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.