ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Ɗage Taronta Bayan Arangamar ‘Yansanda Da ‘Yan Daba A Abuja

by Sadiq
7 months ago
PDP

A ranar Talata, an samu tashin hankali a shalkwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja bayan ‘yan daba daga ɓangarori biyu da ke taƙaddama da juna sun yi artabu a ofishin jam’iyyar.

Rigimar ta fara ne da sassafe lokacin da magoya bayan dakataccen sakataren jam’iyyar, Sanata Samuel Anyanwu, suka iso wajen da misalin ƙarfe 8 na safe.

  • Zaɓen 2027: Malami Zai Fito Takarar Gwamna A  Kebbi
  • ’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

Sun ce sun isa ofishin ne domin karɓar ragamar jam’iyyar bayan gudanar da taron jam’iyyar a makon da ya gabata.

ADVERTISEMENT

Amma magoya bayan shugaban jam’iyyar na riƙon kwarya, Ambasada Umar Damagum, suka taru domin hana su shiga.

Lamarin ya yi ƙamari, inda ‘yan daba daga ɓangarorin biyu suka afka wa juna da faɗa.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

’Yansanda da ke wajen sun yi ƙoƙarin kwantar da tarzomar, duk da cewa manyan jam’iyyar kamar Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, suna wajen.

Daga ƙarshe, ’yansanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa su.

Wannan ya sa ’yan jarida, ma’aikata da mambobin jam’iyyar suka nemi mafaka, yayin da wasu mutane suka ji rauni.

Rikicin ya yi sanadin lalata wasu kadarorin hedikwatar jam’iyyar.

Saboda wannan tashin hankali, sabon shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya sanar da ɗage taron farko na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar (NWC) da aka shirya yi a ranar Talatar.

Da yake magana da ’yan jarida, Turaki ya ce an ɗage taron zuwa ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.

Ya zargi “maƙiyan ci gaba da maƙiyan dimokuraɗiyya” da haddasa rikicin.

Turaki, ya gode wa Kwamishinan ’Yansandan Abuja, saboda samar da tsaro.

Ya kuma yaba wa gwamnoni, ’yan majalisa, tsofaffin ministoci, shugabannin jam’iyya da sauran manyan jam’iyyar saboda goyon bayansu.

Ya ce PDP jam’iyya ce mai son zaman lafiya, kuma dole ta ci gaba da kasancewa a haka domin samun damar kowawa mulki.

Rikicin shugabanci ya ƙara tsananta bayan da jam’iyyar ta kori Samuel Anyanwu, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wasu da ake zargi da cin amanar jam’iyyar.

Magoya bayansu su ma sun shirya yin nasu taron a hedikwatar jam’iyyar a ranar Talata, lamarin da ya ƙara dagula al’amura.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

Ku Hukunta Masu Laifi Ba Tare Da La’akari Da Ƙabila Ko Addini Ba – Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.