• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kutsen Intanet Wani Nau’i Ne Na Ta’addanci

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kutsen Intanet Wani Nau’i Ne Na Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan shafe watanni ana gudanar da bincike, hukumomin kasar Sin sun bankado kutsen da aka yi wa jami’ar kimiyya da fasaha ta arewa maso yammacin kasar wato NPU.

Rahotannin binciken da aka fita a jiya, sun bayyana yadda ofishin tattara bayanan sirri ta intanet na TAO na ma’aikatar tsaron Amurka NSA, ya yi amfani da hanyoyi 41 wajen yi wa jami’ar NPU kutse tare da satar bayanan wasu muhimman fasahohi.

  • Kasar Sin Za Ta Taka Gagarumar Rawa Wajen Tsara Dokoki Da Ka’idojin Cinikayya Na Kasa Da Kasa.

Ta’addanci ba ya nufin daukar makami da kaddamar da hare-hare kadai, kutsen intanet ma wani nau’i ne na ta’addanci, domin irin illolin da zai iya haifarwa da ba za su iya misaltuwa ba.

Kasashe da hukumomi da al’ummomi har ma da daidaikun mutanen duniya sun fi mayar da hankali ne kan gudanar da harkokinsu ta intanet har ma da adana muhimman bayanan sirri, kasancewarta fasaha ta zamani kuma mai saukin amfani.

Sai dai kuma, wasu na daukarta a matsayin makami na liken asiri da tsaiko ga ci gaban kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Kutsen intanet da Amurka ta yi, ya bayyana ainihin abun da take fakewa da shi da sunan tsaron kasa ko intanet.

A ko da yaushe, ta kan fake da tsaron kasa ko intanet, wajen zartar da dokoki marasa ma’ana ko zargin wasu da yi mata kutse, ashe dai, abun da take yi ne take gudun a yi mata, kamar dai yadda ake cewa, “wanzam bai son jarfa”.

Ko a baya-bayan nan, ta hana sayarwa kamfanonin kasar Sin kananan na’urorin laturoni da sunan kiyaye tsaron kasa, wanda wani salo ne da ta bullo da shi domin habaka kasuwar nata kamfanoni.

Hakika wannan yunkuri zai kara tayar da hankalin al’ummomin duniya, domin ya nuna cewa, babu wanda zai iya tsira daga kutsen.

Sam bai dace a ce ana samun irin haka daga kasa kamar Amurka da a kullum take nanata batun tsaron kasa ko kare hakki ko tsaron intanet ba.

Domin bayan aikin ta’addanci, kutse intanet, wani nau’i ne na keta hakkin jama’a da ma tsaron sirrikansu.(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CIFTIS Na Kara Samun Mahalarta

Next Post

Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Tsarin Samun Nasarori A Muhimman Fasahohin Muhimman Bangarori

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

60 minutes ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

3 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

20 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

20 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

22 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Tsarin Samun Nasarori A Muhimman Fasahohin Muhimman Bangarori

Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Tsarin Samun Nasarori A Muhimman Fasahohin Muhimman Bangarori

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Intanet

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.