ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

by Sadiq
10 months ago
Ceto

Rundunar ’Yansandan Jihar Edo, ta ceto mutane 16 da aka sace a wasu hare-hare daban-daban da aka kai a kan titunan Benin zuwa Legas da Benin zuwa Akure.

Kakakin rundunar, Joel Yamu, ya ce nasarar ta samu ne sakamakon haɗin gwiwar ’yansanda da jami’an sa-kai da mafarauta.

  • Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
  • Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Ya bayyana cewa mutane shida aka ceto a kan titin Beninzuwa Akure, ɗaya daga cikinsu ya samu raunin harbin bindiga amma an taimaka masa kuma yanzu ana kula da shi a asibiti.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, mutane uku aka ceto a kan titin Benin zuwa Legas, sai kuma wasu mutane bakwai da aka sace a kan titin Benin zuwa Akure da aka sake su ranar 25 ga watan Agusta.

’Yansanda sun ce masu garkuwa da mutane sun tare titin a ranar 23 ga watan Agusta tsakanin ƙarfe 5:30 zuwa 6:00 na yamma, inda suka yi awon gaba da matafiya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Bayan samum rahotom faruwar lamarin, jami’an tsaro suka bazu cikin dazuka domin ceto waɗanda suka sace.

Kwamishinan ’yansandan jihar, Monday Agbonika, ya jagoranci aikin a kan titin Benin zuwa Akure.

Ya ce sun yi amfani da sabbin fasahohi ciki har da jirage marasa matuƙa, wanda ya taimaka wajen samun nasara.

Agbonika ya yaba wa jami’an ’yansanda, sa-kai, da mafarauta bisa haɗin kai, yana mai cewa wannan haɗin gwiwa shi ne mabuɗin magance manyan laifuka.

Ya tabbatar wa jama’a cewa za su ci gaba da aiki har sai an ceto sauran mutanen da aka sace kuma an kama maharan.

“Mun ƙuduri aniyar kawar da miyagun laifuka daga titunanmu da al’ummominmu, kuma za mu yi amfani da dukkanin kayan aiki na fasaha domin kare rayukan jama’a da matafiya,” in ji kwamishinan.

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Next Post
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.