ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (2)

by Sulaiman
3 weeks ago
ASUU

… ci gaba daga makon da ya gabata.

 

Tarihin Yajin Aikin ASUU.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1980, a lokacin mulkin soja, ƙungiyar ta shiga cikin ƙungiyoyin da ke adawa da gwamnatin soja. Tarihi ya nuna cewa, sakamakon haka, ƙungiyar ta shirya yajin aikinta na farko a shekarar 1988 don neman samun ‘yancin kai ga jami’o’i da albashi mai kyau.

 

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Tasirin tsarin Bankin Duniya (WB) da Asusun Kuɗi na Duniya (IMF) da aka ƙaƙaba wa Nijeriya wanda ya aiwatar da tsarin daidaito na ‘yancin cinikayya na (SAP) shi ya fara sanya ASUU tsunduma yajin aiki. Tsarin ya jefa ma’aikatan ilimi cikin mawuyacin hali saboda rashin aiwatar da Tsarin Albashi na Jami’a.

 

Sakamakon haka, gwamnatin soji a wancan lolaci ta ayyana ASUU a matsayin haramtacciyar ƙungiya a ranar 7 ga Agusta, 1988, kuma aka ƙwace dukkan kadarorinta.

 

Amma bayan wannan yajin aikin, an sake bata lasisinta na ci gaba da zama halastacciyar ƙungiya a shekarar 1990, kuma a ranar 23 ga Agusta, 1992, aka sake haramta ta. A ranar 3 ga Satumba, 1992, aka yi wani zama wanda ya tanadar wa ķungiyar wasu yarjejeniyoyi da ta amince da wasu manufofin ƙungiyar, ciki har da haƙƙin ma’aikata na shiga cikin yarjejeniyar gama gari.

 

A shekarun 1994 da 1996, ASUU ta gudanar da wani yajin aiki don nuna rashin amincewa da gwamnatin soja kan korar ma’aikata da Janar Sani Abacha ya yi.

 

A ranar 17 ga Disamba, 2013, ASUU ta ayyana yajin aikin da ya ɗauki tsawon watanni shida kan rashin aiwatar da yarjejeniyar 2009 tsakaninta da gwamnatin tarayya, wanda daga ƙarshe aka dakatar da yajin aikin bayan da ƙungiyar ta amince da wasu yarjejeniyoyi. Duk da haka, shekara guda bayan haka, ƙungiyar ta ci gaba da yajin aikin gargaɗi na mako guda kan gazawar gwamnati wajen aiwatar da yarjejeniyar 2009 da kuma yarjejeniyar 2013.

 

A cewar ƙungiyar: “Ba a aiwatar da ɓangarori da yawa na yarjejeniyar 2013 da yarjejeniyar 2009 da gwamnatin tarayya ta yi alƙawari ba”. Yarjejeniyar ta haɗa da biyan haƙƙoƙin mambobinta da aka riƙe tun daga Disambar 2015, kuɗaɗen farfaɗo da jami’o’i, tsarin fansho, tsarin tara kudi a asusu ɗaya (TSA) da ‘yancin kai na jami’o’i da sake tattaunawa batun yarjejeniyar 2009 sannan kuma, tsarin manufar gwamnati ta “babu aiki, babu albashi” dole a dakatar da ita.

 

Yajin Aikin ASUU daga 1999 – 2022

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta fuskanci yajin aiki da dama tun daga shekarar 1999, inda aka fi yin yajin aiki a shekarar 2003, 2010, 2013, 2020, da 2022, galibi saboda rashin aiwatar da yarjejeniyoyi da gwamnati ke yi wurin fitar da kuɗaɗen jami’o’i. Yajin aikin da ya fi tsayi ya faru ne a shekarar 2020 (watanni 9) da kuma 2022 (watanni 8).

 

A cewar ASUU, waɗannan yajin aikin, an gudanar da su ne don tilasta wa ɓangaren gwamnati aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma. Don haka, ƙungiyar ta ASUU tana ƙoƙarin matsa wa gwamnati lamba don ɗaukar matakan da suka dace, amma wannan yana yin illa ga ɗaliban jami’o’i.

 

Ga jerin yajin aikin da ƙungiyar ASUU ta gudanar tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya:

1999 – Watanni 5

2001 – Watanni 3

2002 – Makonni 2

2003 – Watanni 6

2005 – Makonni 2

2006 – Kwanaki 3

2007 – Watanni 3

2008 – Mako 1

2009 – Watanni 4

2010 – Watanni 5

2011 – Kwanaki 59

2013 – Watanni 5

2017 – Watanni 1

2018 – Watanni 3

2020 – Watanni 9

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.