ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (2)

by Sulaiman
6 months ago
ASUU

… ci gaba daga makon da ya gabata.

 

Tarihin Yajin Aikin ASUU.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1980, a lokacin mulkin soja, ƙungiyar ta shiga cikin ƙungiyoyin da ke adawa da gwamnatin soja. Tarihi ya nuna cewa, sakamakon haka, ƙungiyar ta shirya yajin aikinta na farko a shekarar 1988 don neman samun ‘yancin kai ga jami’o’i da albashi mai kyau.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tasirin tsarin Bankin Duniya (WB) da Asusun Kuɗi na Duniya (IMF) da aka ƙaƙaba wa Nijeriya wanda ya aiwatar da tsarin daidaito na ‘yancin cinikayya na (SAP) shi ya fara sanya ASUU tsunduma yajin aiki. Tsarin ya jefa ma’aikatan ilimi cikin mawuyacin hali saboda rashin aiwatar da Tsarin Albashi na Jami’a.

 

Sakamakon haka, gwamnatin soji a wancan lolaci ta ayyana ASUU a matsayin haramtacciyar ƙungiya a ranar 7 ga Agusta, 1988, kuma aka ƙwace dukkan kadarorinta.

 

Amma bayan wannan yajin aikin, an sake bata lasisinta na ci gaba da zama halastacciyar ƙungiya a shekarar 1990, kuma a ranar 23 ga Agusta, 1992, aka sake haramta ta. A ranar 3 ga Satumba, 1992, aka yi wani zama wanda ya tanadar wa ķungiyar wasu yarjejeniyoyi da ta amince da wasu manufofin ƙungiyar, ciki har da haƙƙin ma’aikata na shiga cikin yarjejeniyar gama gari.

 

A shekarun 1994 da 1996, ASUU ta gudanar da wani yajin aiki don nuna rashin amincewa da gwamnatin soja kan korar ma’aikata da Janar Sani Abacha ya yi.

 

A ranar 17 ga Disamba, 2013, ASUU ta ayyana yajin aikin da ya ɗauki tsawon watanni shida kan rashin aiwatar da yarjejeniyar 2009 tsakaninta da gwamnatin tarayya, wanda daga ƙarshe aka dakatar da yajin aikin bayan da ƙungiyar ta amince da wasu yarjejeniyoyi. Duk da haka, shekara guda bayan haka, ƙungiyar ta ci gaba da yajin aikin gargaɗi na mako guda kan gazawar gwamnati wajen aiwatar da yarjejeniyar 2009 da kuma yarjejeniyar 2013.

 

A cewar ƙungiyar: “Ba a aiwatar da ɓangarori da yawa na yarjejeniyar 2013 da yarjejeniyar 2009 da gwamnatin tarayya ta yi alƙawari ba”. Yarjejeniyar ta haɗa da biyan haƙƙoƙin mambobinta da aka riƙe tun daga Disambar 2015, kuɗaɗen farfaɗo da jami’o’i, tsarin fansho, tsarin tara kudi a asusu ɗaya (TSA) da ‘yancin kai na jami’o’i da sake tattaunawa batun yarjejeniyar 2009 sannan kuma, tsarin manufar gwamnati ta “babu aiki, babu albashi” dole a dakatar da ita.

 

Yajin Aikin ASUU daga 1999 – 2022

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta fuskanci yajin aiki da dama tun daga shekarar 1999, inda aka fi yin yajin aiki a shekarar 2003, 2010, 2013, 2020, da 2022, galibi saboda rashin aiwatar da yarjejeniyoyi da gwamnati ke yi wurin fitar da kuɗaɗen jami’o’i. Yajin aikin da ya fi tsayi ya faru ne a shekarar 2020 (watanni 9) da kuma 2022 (watanni 8).

 

A cewar ASUU, waɗannan yajin aikin, an gudanar da su ne don tilasta wa ɓangaren gwamnati aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma. Don haka, ƙungiyar ta ASUU tana ƙoƙarin matsa wa gwamnati lamba don ɗaukar matakan da suka dace, amma wannan yana yin illa ga ɗaliban jami’o’i.

 

Ga jerin yajin aikin da ƙungiyar ASUU ta gudanar tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya:

1999 – Watanni 5

2001 – Watanni 3

2002 – Makonni 2

2003 – Watanni 6

2005 – Makonni 2

2006 – Kwanaki 3

2007 – Watanni 3

2008 – Mako 1

2009 – Watanni 4

2010 – Watanni 5

2011 – Kwanaki 59

2013 – Watanni 5

2017 – Watanni 1

2018 – Watanni 3

2020 – Watanni 9

Asuu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.