ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Nemi Tinubu Ya Dakatar Da Haƙar Ma’adinai Na Tsawon Watanni 6

by Sulaiman
3 weeks ago
Gwamnonin Arewa

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) ta bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara da ya umurci Ministan Ma’adanai da ya dakatar da haƙar ma’adinai na tsawon watanni shida domin a ba da damar gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike.

 

Ƙungiyar ta ce ta lura cewa, haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba na zama babban abin da ke haifar da matsalolin tsaro a Arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya karanta, bayan taron haɗin gwiwa na Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa da aka gudanar a Kaduna ranar Litinin, ƙungiyar ta ce ta kafa Asusun tallafin Tsaro na Yankin inda kowace jiha za ta riƙa bayar da gudunmuwar Naira biliyan 1 duk wata-wata a ƙarƙashin tsarin da za a amince da shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

A cewar sanarwar, “Taron yana mika ta’aziyya da goyon baya ga Gwamnatoci da mutanen kirki na jihohin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sokoto, Jigawa da Kano bayan kisan gilla da sace yaran makaranta da sauran ‘yan ƙasa wanda ba su ji ba su gani ba, da kuma waɗanda hare-haren Boko Haram suka shafa a jihohin Borno da Yobe.

 

“Taron yana yaba wa Gwamnatin Tarayya, karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, saboda jajircewa wajen tabbatar da sakin wasu daga cikin yaran da aka sace cikin gaggawa da kuma magance wasu kalubalen tsaro. Haka kuma muna yaba wa sadaukarwar da sojojinmu suka yi wadanda ke ci gaba da yaki da nau’ikan tashe-tashen hankula daban-daban a fadin kasar.

 

“Taron ya sake jaddada goyon bayansa da jajircewarsa ga kafa ‘Yansandan Jiha. Saboda haka, taron yana karfafa wa ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jihohi a yankin da su hanzarta daukar mataki don aiwatar da wannan kudiri,” in ji sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Shugaban Faransa Zai Gudanar Da Ziyarar Aiki A Kasar Sin 

Shugaban Faransa Zai Gudanar Da Ziyarar Aiki A Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.