ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Nemi Tinubu Ya Dakatar Da Haƙar Ma’adinai Na Tsawon Watanni 6

by Sulaiman
9 months ago
Gwamnonin Arewa

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) ta bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara da ya umurci Ministan Ma’adanai da ya dakatar da haƙar ma’adinai na tsawon watanni shida domin a ba da damar gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike.

 

Ƙungiyar ta ce ta lura cewa, haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba na zama babban abin da ke haifar da matsalolin tsaro a Arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya karanta, bayan taron haɗin gwiwa na Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa da aka gudanar a Kaduna ranar Litinin, ƙungiyar ta ce ta kafa Asusun tallafin Tsaro na Yankin inda kowace jiha za ta riƙa bayar da gudunmuwar Naira biliyan 1 duk wata-wata a ƙarƙashin tsarin da za a amince da shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

A cewar sanarwar, “Taron yana mika ta’aziyya da goyon baya ga Gwamnatoci da mutanen kirki na jihohin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sokoto, Jigawa da Kano bayan kisan gilla da sace yaran makaranta da sauran ‘yan ƙasa wanda ba su ji ba su gani ba, da kuma waɗanda hare-haren Boko Haram suka shafa a jihohin Borno da Yobe.

 

“Taron yana yaba wa Gwamnatin Tarayya, karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, saboda jajircewa wajen tabbatar da sakin wasu daga cikin yaran da aka sace cikin gaggawa da kuma magance wasu kalubalen tsaro. Haka kuma muna yaba wa sadaukarwar da sojojinmu suka yi wadanda ke ci gaba da yaki da nau’ikan tashe-tashen hankula daban-daban a fadin kasar.

 

“Taron ya sake jaddada goyon bayansa da jajircewarsa ga kafa ‘Yansandan Jiha. Saboda haka, taron yana karfafa wa ‘yan majalisar dokoki na kasa da na jihohi a yankin da su hanzarta daukar mataki don aiwatar da wannan kudiri,” in ji sanarwar.

Gwamnonin Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • Sulaiman
    Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
Next Post
Shugaban Faransa Zai Gudanar Da Ziyarar Aiki A Kasar Sin 

Shugaban Faransa Zai Gudanar Da Ziyarar Aiki A Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gwamnonin Arewa

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamnonin Arewa

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.