ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

by Sadiq
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Benuwe (SEMA), ta ce akalla mutane 23 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a jihar tun bayan faduwar damina. 

Sakataren zartarwa, Dakta Emmanuel Shior ne, ya sanar da hakan yayin da yake kaddamar da rabon kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a ranar Talata a Makurdi.

  • Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta
  • Adadin Kudin Shigar Kayayyakin Manhajar Masana’antun Sin A Watanni 7 Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 8.7 Bisa Dari

Ya ce mutane 116,084 ne kuma suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa da ta afku a wasu sassan jihar.

ADVERTISEMENT

“Mutane 74 na fama da raunuka daban-daban. 14 daga cikin 23 da sun mutu a sakamakon hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Guma,” inji shi.

Sakataren zartaswar ya kuma bayyana cewa kawo yanzu ambaliyar ta shafi gonaki hekta 14,040 yayin da gidaje 4,411 suka nutse.

LABARAI MASU NASABA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

“Makaranta da kasuwanni, kamfanoni, gidaje da filayen noma da ke yankuna 104 abin ya shafa,” in ji shi.

Ya lissafa kananan hukumomin da abin ya shafa kamar haka, Guma, Vandeikya, Otukpo, Katsina-ala, Makurdi, Apa, Agatu, Tarka, Gboko, Gwer-West da Logo.

“Wadanda abin ya shafa na bukatar agajin gaggawa. Wannan shi ne dalilin wannan aiki namu.

“Mun fara ne da Makurdi da Agatu saboda su ne suke da mutane 34 da 28 da abin ya shafa.

“Wadanda abin ya rutsa da su a Agatu da a halin yanzu suka fake a babbar hanyar tarayya nan ba da jimawa ba za a koma Obagaji,” in ji shi.

Shima da yake jawabi a wajen taron, babban jami’in bincike da ceto na hukumar bada agajin gaggawa ta kasa, John Digah, ya ce hukumar ta tura na’urar kula da ruwa domin tallafa wa wadanda abin ya shafa da ruwan sha.

Digah ya ce na’urar tana da karfin maganin lita 2,000 na ruwa a cikin sa’a guda.

“A cikin kwanaki biyun da suka gabata mun yi jinya tare da raba wa wadanda abin ya shafa ruwan lita 140,000,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki
Labarai

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.