ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Benuwe (SEMA), ta ce akalla mutane 23 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a jihar tun bayan faduwar damina. 

Sakataren zartarwa, Dakta Emmanuel Shior ne, ya sanar da hakan yayin da yake kaddamar da rabon kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a ranar Talata a Makurdi.

  • Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta
  • Adadin Kudin Shigar Kayayyakin Manhajar Masana’antun Sin A Watanni 7 Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 8.7 Bisa Dari

Ya ce mutane 116,084 ne kuma suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa da ta afku a wasu sassan jihar.

ADVERTISEMENT

“Mutane 74 na fama da raunuka daban-daban. 14 daga cikin 23 da sun mutu a sakamakon hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Guma,” inji shi.

Sakataren zartaswar ya kuma bayyana cewa kawo yanzu ambaliyar ta shafi gonaki hekta 14,040 yayin da gidaje 4,411 suka nutse.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

“Makaranta da kasuwanni, kamfanoni, gidaje da filayen noma da ke yankuna 104 abin ya shafa,” in ji shi.

Ya lissafa kananan hukumomin da abin ya shafa kamar haka, Guma, Vandeikya, Otukpo, Katsina-ala, Makurdi, Apa, Agatu, Tarka, Gboko, Gwer-West da Logo.

“Wadanda abin ya shafa na bukatar agajin gaggawa. Wannan shi ne dalilin wannan aiki namu.

“Mun fara ne da Makurdi da Agatu saboda su ne suke da mutane 34 da 28 da abin ya shafa.

“Wadanda abin ya rutsa da su a Agatu da a halin yanzu suka fake a babbar hanyar tarayya nan ba da jimawa ba za a koma Obagaji,” in ji shi.

Shima da yake jawabi a wajen taron, babban jami’in bincike da ceto na hukumar bada agajin gaggawa ta kasa, John Digah, ya ce hukumar ta tura na’urar kula da ruwa domin tallafa wa wadanda abin ya shafa da ruwan sha.

Digah ya ce na’urar tana da karfin maganin lita 2,000 na ruwa a cikin sa’a guda.

“A cikin kwanaki biyun da suka gabata mun yi jinya tare da raba wa wadanda abin ya shafa ruwan lita 140,000,” in ji shi.

MASU ALAKA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina
Labarai

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.