ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta

by Sadiq
4 years ago
APC

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya dage fara yakin neman zaben da aka shirya kaddamarwa a ranar Laraba.

Darakta-Janar na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Shettima, kuma gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

  • Masar Ta Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Na Gwaji A Makarantun Midil Na Kasar
  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

A cewarsa, an yi hakan ne domin daidaita jadawalin lokaci da jadawalin ayyuka ne domin ya yi daidai da harkokin duk masu hannu a cikin yakin neman zaben don samun nasararsa.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon lokacin da za a fara yakin neman zaben jam’iyyar.

Sanarwar ta ce; “Tun da farko mun shirya tattaki da addu’o’in zaman lafiya a ranar Laraba, 28 ga watan Satumba, 2022, don fara yakin neman zaben shugaban kasa na 2023 a hukumance. Mun kuma sanar da cewa mambobin kwamitin yakin neman zaben sun kai rahoto hedikwatar yakin neman zaben a ranar domin karbar wasikun nadi.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

“Duk da haka, saboda fadada jerin sunayen don samun karin masu ruwa da tsaki da bukatun cikin gida a APC, mun yanke shawarar daidaita jadawalin wadannan ayyuka domin tabbatar da cewa kowa yana cikin jirgin kafin a fara ayyukan a hukumance.

“Saboda haka, ayyukan da aka sanar a baya na ranar 28 ga Satumba ba za su ci gaba da kasancewa ba.

“A matsayinmu na jam’iyya mai mulki kuma mafi inganci a Nijeriya, mun fahimci sadaukarwa da fahimtar dimbin mambobinmu wadanda suka fi son sadaukar da kansu don wannan gagarumin aiki da ke gabanmu. Hakan kuma ya nuna irin tsananin soyayyar da ‘ya’yan jam’iyyar ke yi wa ’yan takararmu

“Za a sanar da sabon kwanan wata da jadawalin abubuwan da za su faru nan ba da jimawa ba”.

Idan ba a manta ba ranar 28 ga watan Satumba, 2022, ita ce ranar da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), ta ware ta ga jam’iyyu da ‘yan takara don fara yakin neman zabe a hukumance.

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.