• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bana An Noma Masara Da Tsadar Gaske – Makarfi

by Abubakar Abba
3 years ago
Masara

Shugaban kungiyar manoman masara don samun riba na yankin Arewa maso gabas Alhaji Adamu Muhammad Makarfi, ya sanar da cewa, a bana, an yi noman masara da tsadar gaske, saboda tashin farashin takin zamani, inda kudin buhu daya ya kai kusan naira 30,000.

Adamu a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a kaduna ya ce, sabin yadda ake sayar da takin kan naira 5,000 a baya, a bana farashinsa ya ninka, inda ya ce, hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe ciyawa da kudin kwadago, sun karu.

  • Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…
  • Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi

Ya ci gaba da cewa, haka ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin kasar nan kamar su Zamfara da Sakkwato da Jigawa da Katsina da kaduna da wasu jihohin duk an samu wannan iftila’in, inda hakan ya jawo wa manoma yin asara.

Ya kara da cewa, “A matsayina, na manomi mu bukatar mu ba wai a sayar da amfanin gona da tsada a kasar nan ba, amma duk da haka, ba za mu so ace manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma, asara ce ga kasa baki daya”.

Ya yi nuni da cewa, domin duk inda aka ce manomi ya yi noma kuma ya fadi, babban abin da ake jin tsaro, musamman manyan manoma da yawancin su suke yi don riba in sun fadi akwai matsala domin akasarin suna ciwo bashi ne a banki domin yin noma da kuma kudin ruwan da ake dora masu, asarar za ta yi masu yawa.

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Adamu ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi nom aba a kasar nan, za samu karancin abinci, inda ya ce, hakan ne ya sa zaka ga ana yin kira aje a sawo abinci daga ketare, in an sawo abincin daga ketare, Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa domin hakan zai iya dfurkusar da tattalin arzikin kasar nan.

Ya yi nuni da cewa, misali an je an sawo tan miliyan biyu na masara don shigo wa da shi cikin Nijeriya, sai an kashe kusan naira tiriliyan daya, inda ya kara da cewa, a kasar nan, ban da sauran amfanin gona kasar nan na bukatar akalla tan miliyan ashirin.

Ya ce, in har za a sawo masara a kasar waje ba a noma a kasar nan ba, akalla za mu yi asarar zunzurutun kudi kamar naira tirilyan goma, inda yay i nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar taimakon da ya dace, ba karamar matsala ce za ta auku ba.

Ya yi kira musamman ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da na kananan hukumomi su mayar da hankali kan bunkasa noman rani, inda ya yi nuni da cewa, ya zama wajibi a samar da kyakyawan tsari, amma idan ba a yi hakan ba, ba mu san irin abin da zai faru a kasar nan ba.

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi, na dakile ‘yan kasuwa na kasar waje zuwa gonakan manoman kasar nan don sayen amfanin gona da suka noma kai tsaye, Makarfi ya ce, wannan tsarina bin yaba wa ne, sai ya sanar da gwamnatin ta makaro domin tun tuni ya kamata a ce an yi irin wannan tsarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Ibrahim Gusau Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Nijeriya

Da Dumi-Dumi: Ibrahim Gusau Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.