• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bana An Noma Masara Da Tsadar Gaske – Makarfi

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Bana An Noma Masara Da Tsadar Gaske – Makarfi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar manoman masara don samun riba na yankin Arewa maso gabas Alhaji Adamu Muhammad Makarfi, ya sanar da cewa, a bana, an yi noman masara da tsadar gaske, saboda tashin farashin takin zamani, inda kudin buhu daya ya kai kusan naira 30,000.

Adamu a hirarsa da LEADERSHIP Hausa a kaduna ya ce, sabin yadda ake sayar da takin kan naira 5,000 a baya, a bana farashinsa ya ninka, inda ya ce, hatta magungunan feshi na kwari ko na kashe ciyawa da kudin kwadago, sun karu.

  • Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…
  • Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi

Ya ci gaba da cewa, haka ambaliyar ruwan sama da aka samu a wasu jihohin kasar nan kamar su Zamfara da Sakkwato da Jigawa da Katsina da kaduna da wasu jihohin duk an samu wannan iftila’in, inda hakan ya jawo wa manoma yin asara.

Ya kara da cewa, “A matsayina, na manomi mu bukatar mu ba wai a sayar da amfanin gona da tsada a kasar nan ba, amma duk da haka, ba za mu so ace manoma sun yi asara ba, domin asarar manoma, asara ce ga kasa baki daya”.

Ya yi nuni da cewa, domin duk inda aka ce manomi ya yi noma kuma ya fadi, babban abin da ake jin tsaro, musamman manyan manoma da yawancin su suke yi don riba in sun fadi akwai matsala domin akasarin suna ciwo bashi ne a banki domin yin noma da kuma kudin ruwan da ake dora masu, asarar za ta yi masu yawa.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Adamu ya ci gaba da cewa, idan manyan manoma ba su yi nom aba a kasar nan, za samu karancin abinci, inda ya ce, hakan ne ya sa zaka ga ana yin kira aje a sawo abinci daga ketare, in an sawo abincin daga ketare, Nijeriya za ta iya yin asara mai yawa domin hakan zai iya dfurkusar da tattalin arzikin kasar nan.

Ya yi nuni da cewa, misali an je an sawo tan miliyan biyu na masara don shigo wa da shi cikin Nijeriya, sai an kashe kusan naira tiriliyan daya, inda ya kara da cewa, a kasar nan, ban da sauran amfanin gona kasar nan na bukatar akalla tan miliyan ashirin.

Ya ce, in har za a sawo masara a kasar waje ba a noma a kasar nan ba, akalla za mu yi asarar zunzurutun kudi kamar naira tirilyan goma, inda yay i nuni da cewa, idan ba a bai wa manoman kasar taimakon da ya dace, ba karamar matsala ce za ta auku ba.

Ya yi kira musamman ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da na kananan hukumomi su mayar da hankali kan bunkasa noman rani, inda ya yi nuni da cewa, ya zama wajibi a samar da kyakyawan tsari, amma idan ba a yi hakan ba, ba mu san irin abin da zai faru a kasar nan ba.

Da yake yin tsokaci kan tsarin da gwamnatin tarayya ta fito da shi, na dakile ‘yan kasuwa na kasar waje zuwa gonakan manoman kasar nan don sayen amfanin gona da suka noma kai tsaye, Makarfi ya ce, wannan tsarina bin yaba wa ne, sai ya sanar da gwamnatin ta makaro domin tun tuni ya kamata a ce an yi irin wannan tsarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ManomaMasaraNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Next Post

Da Dumi-Dumi: Ibrahim Gusau Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Nijeriya

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Ibrahim Gusau Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Nijeriya

Da Dumi-Dumi: Ibrahim Gusau Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.