ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi

by Leadership Hausa
4 years ago
Neman Gwamnatin Tarayya

Jihohi uku, da suka hada da Ebonyi, Gombe da kuma Nasarawa sun mika bukatar gwamnatin tarayya ta karbi harkokin gudanar da filayen jiragen saman jihohin su, bukatar da gwamnati ta amince da ita. Wannan kuma yana nufin cewa, a ‘yan kwanaki masu zuwa dole gwamnatin tarayya ta amayo wasu biliyoyin nairori don mayar wa da gwamnatocin wadannan jihohin, misali a nan shi ne gwamnatin Jihar Nasarawa ta mika bukatar Naira Biliyan 10 ga gwamnatin tarayya na karbar ragamar filin jiragen sama dana daukar manya kaya na garin Lafia da ke Jihar Nasarawar.

Babban abin da ya kamata a fahimta a nan shi ne wadannanfilayen jiragen sama da aka gina a jihohin nan uku duk an yi sune da manufar siyasa kawai ba wai don wani buri na bunkasar tattalin arziki ba.

  • Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 

Muna wannan bayanin ne don tunda farko akwai filayen jiragen sama da al’ummar wadannan jihohin za su iya amfani da su ba tare da wata matsala ba, misali, jihar Ebonyi za ta iya a cikin sauki da filin jiragen sama na garin Inugu; Jihar Gombe za ta iya amfani da na garin Bauchi yayin da filin jirgin sama na jihar Benuwai zai iya zama abin amfani ga al’umma JIhar Nasarawa.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa, ana sa ran filayen jiragen saman su samar da kudin shiga amma bincikenmu ya nuna cewa, cikin filayen jiragen sama 22 da muke da su a Nijeriya filayen jirgin sama na Legas, Fatakwal, Kano da kuma Abuja ne kawai kuma wadanda dukkansu hukumar Kula da filayen jiragen saman ta Nijeriya ke kula da su kadai ke samar da kudin shigar da za a iya magana a kai.

A ra’ayin wannan jaridar, shawarar wasu gwamnonin jihohi ta samar da filayen jiragen sama abu ne da ba zai haifar da da mai ido ba. Yawanci su suna gina filayen ne don cimma wani buri na kashin kansu. Wanann kuma abin takaici ne in har muka lura da cewa, gina filin Jirgin sama abu ne da yake bukatar dinbin kudade masu yawan gaske.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Mai zai sa jihar da take rarrafe tare da neman kudaden gudanar da ayyukanta za ta fara kaddamar da gina filin Jirgin sama tun da farko? Wannan kamar an yi ne kawai don biyan bukatar wasu kalilan daga cikin al’ummar jihar masu hannun da shuni, maimakon a karkatar da kudaden wajen samar da hanyoyin warware matsalolin da al’umma ke fuskanta na rashin Ruwan sha da hanyoyi da wutar lanytar da sauran ababen more rayuwa da mafi yawan mutanen jihohin ke fuskanta.

A bayyana yake cewa, gwamnatin Jihar Ebonyi ta yanzu da gwamnatocin da suka shude a jihohin Gombe da Nasarawa ba su yi bincike na yadda kamata ba kafin su tsiri fara gina filayen jirgin sama a yankunan nasu, da gwamnatocin wadannan jihohin sun yi wannan bincike da basu kai yin haka ba don yin wannan aikin tamkar rashin sanin abin da ya kamata a muhimmantar da shi ne a rayuwar al’umma gaba daya.

Idan za a yi adalci ga GwamnaAbdullahi Sule da Gwamna Muhammadu Yahaya, wadanda suka gada Tsofaffin gwamnonin jihohin da suka hada da Umaru Tanko Al-Makura da Danjuma Goje sune suka kirkiri gina filayen jiragen saman a jihohin Nasarawa da Gombe.

Ana iya cewa, ba zai yiwu Gwamna Sule da Gwamna Yahaya, wadanda dukkan su ‘yan kasuwa ne su rungumi irin wannan harkar ta samar da filayen sama tun da farko ba.

Amma ga Gwamnan jihar Ebonyi, Dabe Umahi wannan kamar wani babbar rashinm muhimmantar da abin da al’umma ke bukata ne. Ba tare da la’akari da yadda jihar za ta fuskanci kula da filin jirgin sama ba kawai sai ya fada gina filin jirgin sama na kasa da kasa, sai kuma ga shi wai yana neman gwamnatin tarayya da ta karbi ragamar gudanar da filin jirgin, wanda ya gada tsohon gwamna Dakta Sam Egwu ya yi irin wannan kuskuren inda ya gina katafariyar cibiyar masana’antu a garin Abakaliki wadda al’umma suka rasa cikakken amfaninta.

Idan za a iya tunawa a shekarar da ta gabata ne Gwamna Umahi ya rubuta wa gwamnatin tarayya bukatar neman bashin Naira Biliyan 10 don sayen kayayyakin aiki na filin jirgin sama, yana mai cewa, da zarar an kamala aikin za su mika filin jirgin ne ga gwamnatin tarayya.

Kwanaki ne kuma Gwamna Umahi ya sanar da gina gidan gwamnatin jihar a kan kudi Naira Biliyan 1.2 a garin Abuja wannan ma wani aikin baban giwa ne.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, in har gwamnatin tarayya ta kuskura ta karbi ragamar wadannan filayen jiragen saman to kamar ta ba wasu jihohi damar shiga sahun irin wadannan aikin ne na baban giwa da ba zai yi wa al’umma amfanin komai ba.

Neman Gwamnatin Tarayya
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Neman Gwamnatin Tarayya
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Neman Gwamnatin Tarayya
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Yadda ‘Yan Nijeriya Za Su Kauce Wa Komawa ‘Yar Gidan Jiya A Zaben 2023

Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.