ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi

by Leadership Hausa
4 years ago
Neman Gwamnatin Tarayya

Jihohi uku, da suka hada da Ebonyi, Gombe da kuma Nasarawa sun mika bukatar gwamnatin tarayya ta karbi harkokin gudanar da filayen jiragen saman jihohin su, bukatar da gwamnati ta amince da ita. Wannan kuma yana nufin cewa, a ‘yan kwanaki masu zuwa dole gwamnatin tarayya ta amayo wasu biliyoyin nairori don mayar wa da gwamnatocin wadannan jihohin, misali a nan shi ne gwamnatin Jihar Nasarawa ta mika bukatar Naira Biliyan 10 ga gwamnatin tarayya na karbar ragamar filin jiragen sama dana daukar manya kaya na garin Lafia da ke Jihar Nasarawar.

Babban abin da ya kamata a fahimta a nan shi ne wadannanfilayen jiragen sama da aka gina a jihohin nan uku duk an yi sune da manufar siyasa kawai ba wai don wani buri na bunkasar tattalin arziki ba.

  • Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 

Muna wannan bayanin ne don tunda farko akwai filayen jiragen sama da al’ummar wadannan jihohin za su iya amfani da su ba tare da wata matsala ba, misali, jihar Ebonyi za ta iya a cikin sauki da filin jiragen sama na garin Inugu; Jihar Gombe za ta iya amfani da na garin Bauchi yayin da filin jirgin sama na jihar Benuwai zai iya zama abin amfani ga al’umma JIhar Nasarawa.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa, ana sa ran filayen jiragen saman su samar da kudin shiga amma bincikenmu ya nuna cewa, cikin filayen jiragen sama 22 da muke da su a Nijeriya filayen jirgin sama na Legas, Fatakwal, Kano da kuma Abuja ne kawai kuma wadanda dukkansu hukumar Kula da filayen jiragen saman ta Nijeriya ke kula da su kadai ke samar da kudin shigar da za a iya magana a kai.

A ra’ayin wannan jaridar, shawarar wasu gwamnonin jihohi ta samar da filayen jiragen sama abu ne da ba zai haifar da da mai ido ba. Yawanci su suna gina filayen ne don cimma wani buri na kashin kansu. Wanann kuma abin takaici ne in har muka lura da cewa, gina filin Jirgin sama abu ne da yake bukatar dinbin kudade masu yawan gaske.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Mai zai sa jihar da take rarrafe tare da neman kudaden gudanar da ayyukanta za ta fara kaddamar da gina filin Jirgin sama tun da farko? Wannan kamar an yi ne kawai don biyan bukatar wasu kalilan daga cikin al’ummar jihar masu hannun da shuni, maimakon a karkatar da kudaden wajen samar da hanyoyin warware matsalolin da al’umma ke fuskanta na rashin Ruwan sha da hanyoyi da wutar lanytar da sauran ababen more rayuwa da mafi yawan mutanen jihohin ke fuskanta.

A bayyana yake cewa, gwamnatin Jihar Ebonyi ta yanzu da gwamnatocin da suka shude a jihohin Gombe da Nasarawa ba su yi bincike na yadda kamata ba kafin su tsiri fara gina filayen jirgin sama a yankunan nasu, da gwamnatocin wadannan jihohin sun yi wannan bincike da basu kai yin haka ba don yin wannan aikin tamkar rashin sanin abin da ya kamata a muhimmantar da shi ne a rayuwar al’umma gaba daya.

Idan za a yi adalci ga GwamnaAbdullahi Sule da Gwamna Muhammadu Yahaya, wadanda suka gada Tsofaffin gwamnonin jihohin da suka hada da Umaru Tanko Al-Makura da Danjuma Goje sune suka kirkiri gina filayen jiragen saman a jihohin Nasarawa da Gombe.

Ana iya cewa, ba zai yiwu Gwamna Sule da Gwamna Yahaya, wadanda dukkan su ‘yan kasuwa ne su rungumi irin wannan harkar ta samar da filayen sama tun da farko ba.

Amma ga Gwamnan jihar Ebonyi, Dabe Umahi wannan kamar wani babbar rashinm muhimmantar da abin da al’umma ke bukata ne. Ba tare da la’akari da yadda jihar za ta fuskanci kula da filin jirgin sama ba kawai sai ya fada gina filin jirgin sama na kasa da kasa, sai kuma ga shi wai yana neman gwamnatin tarayya da ta karbi ragamar gudanar da filin jirgin, wanda ya gada tsohon gwamna Dakta Sam Egwu ya yi irin wannan kuskuren inda ya gina katafariyar cibiyar masana’antu a garin Abakaliki wadda al’umma suka rasa cikakken amfaninta.

Idan za a iya tunawa a shekarar da ta gabata ne Gwamna Umahi ya rubuta wa gwamnatin tarayya bukatar neman bashin Naira Biliyan 10 don sayen kayayyakin aiki na filin jirgin sama, yana mai cewa, da zarar an kamala aikin za su mika filin jirgin ne ga gwamnatin tarayya.

Kwanaki ne kuma Gwamna Umahi ya sanar da gina gidan gwamnatin jihar a kan kudi Naira Biliyan 1.2 a garin Abuja wannan ma wani aikin baban giwa ne.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, in har gwamnatin tarayya ta kuskura ta karbi ragamar wadannan filayen jiragen saman to kamar ta ba wasu jihohi damar shiga sahun irin wadannan aikin ne na baban giwa da ba zai yi wa al’umma amfanin komai ba.

Neman Gwamnatin Tarayya
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Yadda ‘Yan Nijeriya Za Su Kauce Wa Komawa ‘Yar Gidan Jiya A Zaben 2023

Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.