• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NCCE

Hukumar kula da Kwalejojin Ilimi a Nijeriya (NCCE) ta rufe tare da kulle cibiyoyin ilimi guda 41 da ke bada shaidar karatun ilimi ta NCE na bogi a jihar Bauchi.

A wata wasika da hukumar ta aike wa kwamishinan ilimi na jihar Bauchi Dakta Aliyu Usman Tilde Mai dauke da kwanan wata 5 ga watan Satumba 2022 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Laraba, na cewa dukkanin cibiyoyin ilimi da Kwalejojin da lamarin ya shafa an ba su wata daya tak da su tabbatar sun kulle ko kuma su fuskanci shari’a.

  • Hukumar Kula Da Kwalejin Kimiyya Ta Amince Da Sabbin Kwasakwasai 37 A Kwalejin Bida

Wasikar wacce babban sakataren hukumar mai cikakken iko na NCCE, Farfesa Paulinus Chijioke Okwelle ya sanya wa hannu, ya yi tilawar cewa a watan Oktoba da Nuwamban 2021 hukumar ta gudanar da wani atisayen zagayen kwalejoji a fadin kasar nan domin bankado makarantun da ke bada shaidar kammala karatun NCE na bogi, inda a bisa hadin kai jihohi aka samu nasarar gudanar da aikin binciken cikin nasara.

A cewar hukumar NCCE an tura wa ma’aikatar ilimi ta tarayya rahoton aikin binciken da aka gudanar sannan kuma aka bai wa hukumar umarnin ta gaggauta kulle dukkanin cibiyoyin da ta gano na bogi ne.

“Kan wannan, hukumar nan tana jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta taimaka mana wajen tabbatar da wadannan makarantun sun kasance a kulle da suke bayar da shaidar NCE na bogi,” Okwelle ya kara.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

NCCE ta jero sunan kwalejoji da cibiyoyin ilimin da wannan kullewar ta shafa da aka gano suna gudanuwa ta haramtacciyar hanya da cewa su ne kwalejin ilimi Mayo Belwa da ke hadin guiwa da kwalejin ilimi ta Azare; kwalejin ilimi ta Abubakar Adamu Mu’azu da ke Boto; Al-Iman College of Education, Nasarawa. Nasarawa, Bauchi, da kwalejin ilimi ta Apex da ke Liman Katagun, Bauchi.

Sauran sun kunshi kwalejin ilimi da ke Bununu a karamar hukumar Tafawa Balewa; kwalejin ilimi mai zurfi da ke Magama, Gumau, Toro; kwalejin koyar da ilimin larabci da addini da ke Toro; kwalejin SACH da ke Bauchi, makarantar koyar da ilimin Kimiyyar lafiyar muhalli (EHS) da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta ECWA da ke Bayarw da kuma cibiyar ilimi ta Garba Ibrahim.

Cibiyoyin ilimin da rufewar ta shafa har da cibiyar koyar da ilimin addini da larabci ta Murkazul Islam da ke Azare; Azare Sahib College of Education; kwalejin ilimi ta Sardauna da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta Sheikh Adamu Abubakar da ke Azare; Sunnah Bauchi College of Education, Toro; Thomas Moor Institute, Bauchi; Urat Memorial College of Education, Bauchi; Diamond Teachers Training College of Education, Bauchi da kuma kwalejin ilimi ta Ibrahim Bello da ke Magama Gumau.

Sauran sun hada da kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke Bauchi; kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke karamar hukumar Katagum; kwalejin ilimi da ke Burra Ningi; Annur Kano College of Education, Giade; kwalejin Sheikh Adam, Azare, Bauchi; Annur Kano College of Education da ke karamar hukumar Warji; Da’awa Bauchi College of Education, Darazo; Da’awa Bauchi College of Education, Kafin Kafin Madaki, Bauchi; Danyaya College of Education, Miya Ganjuwa Miya Ganjuwa LGA, Bauchi; Darazo College of Education, Akuyam; Gindiri College of Education, Warji LGA, da kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi Kumbotso Gidan Marayu Katagum Zaki.

Farfesa Okwelle, “Dangane da wannan matakin, kwalejoji da cibiyoyin da lamarin nan ya shafa suna da zarafin wata daya da su kulle ko su fuskanci shari’a.”

LEADERSHIP ta yi tilawar cewa a watan July na 2021 Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta nuna damuwarka kan cibiyoyin da aka gano suna bada shaidar kammala karatun NCE na bogi a jihar.

A kudirin da mambar Majalisar mai wakiltar mazabar Hardawa, Hon. Mohammed Babayo ya gabatar, ya ce wannan lamarin na shafan harkar ilimi a jihar tare da gurbata sashin ilimi.

A cewarsa, cikin kwalejin ilimi masu zaman kansu guda 58 da ke bada shaidar kammala NCE, guda 13 ne kacal suke da rijista da NCCE.

Majalisar ta bukaci Gwamnatin jihar Bauchi da ta tuntubi hukumar NCCE da hukumar NBTE domin lalubo bakin zaren dakile makarantun da suke bada shaidar NCE na bogi a jihar.

A cewarsa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a shawo kannwan matsalar domin tsarkake harkokin ilimi.”

Nan take, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Y Sulaiman ya umarci kwamitin Majalisar na ilimi da ya bincike lamarin sannan ya gabatar musu da rahoto cikin kwanaki 30.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.