ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NCCE

Hukumar kula da Kwalejojin Ilimi a Nijeriya (NCCE) ta rufe tare da kulle cibiyoyin ilimi guda 41 da ke bada shaidar karatun ilimi ta NCE na bogi a jihar Bauchi.

A wata wasika da hukumar ta aike wa kwamishinan ilimi na jihar Bauchi Dakta Aliyu Usman Tilde Mai dauke da kwanan wata 5 ga watan Satumba 2022 da wakilinmu ya ci karo da ita a ranar Laraba, na cewa dukkanin cibiyoyin ilimi da Kwalejojin da lamarin ya shafa an ba su wata daya tak da su tabbatar sun kulle ko kuma su fuskanci shari’a.

  • Hukumar Kula Da Kwalejin Kimiyya Ta Amince Da Sabbin Kwasakwasai 37 A Kwalejin Bida

Wasikar wacce babban sakataren hukumar mai cikakken iko na NCCE, Farfesa Paulinus Chijioke Okwelle ya sanya wa hannu, ya yi tilawar cewa a watan Oktoba da Nuwamban 2021 hukumar ta gudanar da wani atisayen zagayen kwalejoji a fadin kasar nan domin bankado makarantun da ke bada shaidar kammala karatun NCE na bogi, inda a bisa hadin kai jihohi aka samu nasarar gudanar da aikin binciken cikin nasara.

ADVERTISEMENT

A cewar hukumar NCCE an tura wa ma’aikatar ilimi ta tarayya rahoton aikin binciken da aka gudanar sannan kuma aka bai wa hukumar umarnin ta gaggauta kulle dukkanin cibiyoyin da ta gano na bogi ne.

“Kan wannan, hukumar nan tana jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta taimaka mana wajen tabbatar da wadannan makarantun sun kasance a kulle da suke bayar da shaidar NCE na bogi,” Okwelle ya kara.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

NCCE ta jero sunan kwalejoji da cibiyoyin ilimin da wannan kullewar ta shafa da aka gano suna gudanuwa ta haramtacciyar hanya da cewa su ne kwalejin ilimi Mayo Belwa da ke hadin guiwa da kwalejin ilimi ta Azare; kwalejin ilimi ta Abubakar Adamu Mu’azu da ke Boto; Al-Iman College of Education, Nasarawa. Nasarawa, Bauchi, da kwalejin ilimi ta Apex da ke Liman Katagun, Bauchi.

Sauran sun kunshi kwalejin ilimi da ke Bununu a karamar hukumar Tafawa Balewa; kwalejin ilimi mai zurfi da ke Magama, Gumau, Toro; kwalejin koyar da ilimin larabci da addini da ke Toro; kwalejin SACH da ke Bauchi, makarantar koyar da ilimin Kimiyyar lafiyar muhalli (EHS) da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta ECWA da ke Bayarw da kuma cibiyar ilimi ta Garba Ibrahim.

Cibiyoyin ilimin da rufewar ta shafa har da cibiyar koyar da ilimin addini da larabci ta Murkazul Islam da ke Azare; Azare Sahib College of Education; kwalejin ilimi ta Sardauna da ke Bauchi; kwalejin ilimi ta Sheikh Adamu Abubakar da ke Azare; Sunnah Bauchi College of Education, Toro; Thomas Moor Institute, Bauchi; Urat Memorial College of Education, Bauchi; Diamond Teachers Training College of Education, Bauchi da kuma kwalejin ilimi ta Ibrahim Bello da ke Magama Gumau.

Sauran sun hada da kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke Bauchi; kwalejin ilimin addini da larabci ta Annur Kano da ke karamar hukumar Katagum; kwalejin ilimi da ke Burra Ningi; Annur Kano College of Education, Giade; kwalejin Sheikh Adam, Azare, Bauchi; Annur Kano College of Education da ke karamar hukumar Warji; Da’awa Bauchi College of Education, Darazo; Da’awa Bauchi College of Education, Kafin Kafin Madaki, Bauchi; Danyaya College of Education, Miya Ganjuwa Miya Ganjuwa LGA, Bauchi; Darazo College of Education, Akuyam; Gindiri College of Education, Warji LGA, da kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi Kumbotso Gidan Marayu Katagum Zaki.

Farfesa Okwelle, “Dangane da wannan matakin, kwalejoji da cibiyoyin da lamarin nan ya shafa suna da zarafin wata daya da su kulle ko su fuskanci shari’a.”

LEADERSHIP ta yi tilawar cewa a watan July na 2021 Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta nuna damuwarka kan cibiyoyin da aka gano suna bada shaidar kammala karatun NCE na bogi a jihar.

A kudirin da mambar Majalisar mai wakiltar mazabar Hardawa, Hon. Mohammed Babayo ya gabatar, ya ce wannan lamarin na shafan harkar ilimi a jihar tare da gurbata sashin ilimi.

A cewarsa, cikin kwalejin ilimi masu zaman kansu guda 58 da ke bada shaidar kammala NCE, guda 13 ne kacal suke da rijista da NCCE.

Majalisar ta bukaci Gwamnatin jihar Bauchi da ta tuntubi hukumar NCCE da hukumar NBTE domin lalubo bakin zaren dakile makarantun da suke bada shaidar NCE na bogi a jihar.

A cewarsa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a shawo kannwan matsalar domin tsarkake harkokin ilimi.”

Nan take, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Y Sulaiman ya umarci kwamitin Majalisar na ilimi da ya bincike lamarin sannan ya gabatar musu da rahoto cikin kwanaki 30.

NCCE
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.