ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

by Sadiq
3 years ago
Maganin Gargajiya

Dubun wani mutum ta cika bayan da aka cafke shi yana sayar wa mutane garin katako da siminti a matsayin maganin gargajiya.

Wata majiya ta rawaito cewa ‘yansanda sun gano mutumin yana hada garin katako da garin farin simintin inda yake sayar wa mutane a matsayin maganin ciwon zazzabin cizon sauro da sauransu.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsohon Atoni-Janar Na Legas Bisa Laifin Karkatar Da Kudade
  • Gwamnatin Tarayya Ta Shiga Tsakani Kan Rikicin Da Ya Kunno Kai Tsakanin Gwamnatin Kogi Da Dangote

A wani bidiyon da aka yi wa mutumin bayan ya shiga hannu, ya ce “Garin katako nake hadawa da garin siminti da kuma garin gypsum da ake yin POP da shi nake kullawa a leda ina sayar wa mutane a matsayin maganin cutar maleriya da sauran cututtuka.

ADVERTISEMENT

“Ina zuwa kasuwanni daban-daban ina sayarwa kuma mutane suna yawan saya.

“Ba ni da kayyadajjen farashin da nake sayarwa, kawai ya danganta da yadda ciniki ya kaya.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

“Na san yana da hatsari, amma saboda yanayin matsayin rayuwar da kasa ke ciki shi ya sa nake yin hakan.”

Wata mata mai suna Taibat, da ke zaune a unguwar Gerewu, ta ce wanda ake zargin yana yawan zuwa kasuwar Mandate da ke Ilori yana sayar da garin, kafin dubunsa ta cika.

Taibat, ta yi kira ga jama’a da su kara lura, sannan ta bukaci gwamnati ta dauki kwararan matakai, inda ta ce Allah ne kadai ya san irin lahanin da garin maganin ya yi wa mutanen da suka yi amfani da shi.

Sai dai kakakin ’yansandan Jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya ce ba shi da labarin faruwar lamarin.

Amma duk da haka, kakakin ’yansandan ya ce da zarar an sanar da ’yansanda za su dauki mataki.

Idan ba a manta ba a baya-bayan nan hukumar NAFDAC sai da ta yi gargadi kan amfani da wasu magaunguna musamman wanda suke da alaka da gargajiya, inda ta ce suna da hatsari ga lafiyar mutane.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina
Al'ajabi

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

November 25, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Next Post
Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro - Atiku

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.