• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Siyasa
0
Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta kaddamar da gangamin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasarta a Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom, inda ta bayyana cewar jam’iyyar APC da ke mulki ta kassara kasar nan.

Jam’iyyar ta bada tabbacin cewa, dan takararta na shugaban kasa, Atiku Abubakar da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa, sun shirya tsaf domin shawo kan matsalolin da kasar nan ke fuskanta.

  • Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsohon Atoni-Janar Na Legas Bisa Laifin Karkatar Da Kudade

Atiku, wanda ya amshi tutar takarar shugaban kasa daga hannun shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu, ya ce kusan kowane fanni a kasar nan ya lalace ga kuma uwa-uba matsalar tsaro da ta addabi kowane dan kasa.

Ya ce a lokacin da yake mataimakin shugaban kasa a 1999, ta za ma kasa mai bunkasar tattalin arziki da ta fi kowace kasa a Afirika, ingataccen tsaro, samar da ayyukan yi, da sauran abubuwan ci gaba da suka samar, ya bada tabbacin samar da fiye da wadannan muddin aka zabe su a 2023.

“Na rantse, idan aka zabi PDP, matsalar tsaro za ta zama tarihi, za a samar wa matasanmu ayyukan yi, harkokin ilimi za su daidaita,” a cewar Atiku.

Labarai Masu Nasaba

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa

Shi kuma a bangarensa abokin takarar Atiku, gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, ya ce a shirye suke su hidimta wa kasar nan, kana ya ce PDP tana da kyawawan tsare-tsare na shawo kan tilin matsalolin da suke addabar kasar nan.

“PDP ita ce jam’iyya daya tilo da ta shirya ceto Nijeriya.

Ya kara da cewa, “Atiku gogaggen dan siyasa ne, dan kasuwa ne da zai iya kyautata tattalin arziki da ci gaban kasar nan muddin aka ba shi dama a 2023.”

Tags: APCAtikuMatsalar TsaroOkowaPDPSiyasaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

Next Post

Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

Related

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida
Siyasa

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida

21 hours ago
Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa
Siyasa

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa

1 day ago
Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano

3 days ago
Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa
Siyasa

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa

6 days ago
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa
Siyasa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

7 days ago
‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
Siyasa

‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

7 days ago
Next Post
Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

Dakarun Soji Sun Kashe 'Yan Ta'addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.