• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakatarorin tsaron Amurka da na Rasha sun tattauna ta wayar tarho, a wani yunkuri na ba kasafai ake mu’amala ba tsakanin kasashen biyu tun bayan da Rasha ta mamaye Ukraine.

Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin da takwaransa na Rasha Sergei Shoigu sun gana ne a ranar Juma’a, kamar yadda kasashen biyu suka tabbatar.

  • Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
  • DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Bangarorin biyu sun ce an tattauna ne kan halin da ake ciki a Ukraine.

Wannan dai shi ne karo na farko da kasashen biyu suka bayar da bayanin wata tattaunawa tun ranar 13 ga Mayu 2022.

Bayan tattaunawar ta ranar Juma’a, ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta ce Mista Austin “ya jaddada muhimmancin kiyaye layukan sadarwa a Ukraine”.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Ma’aikatar tsaron Rasha kuwa ta ce “an tattauna batutuwan da suka shafi tsaron kasa da kasa ciki har da halin da ake ciki a Ukraine”.

Bayan tattaunawar da suka yi a baya a watan Mayu, Mista Austin ya bukaci takwaransa da ya kira tsagaita bude wuta cikin gaggawa, ko da yake Amurka ba ta ambaci bukatar ba a wannan karon.

Hakan dai na zuwa ne bayan da shugaban Kasar Rasha, Vladimir Putin ya bayyana cewa watakila a shirye yake ya yi amfani da makaman nukiliya a Ukraine, da kuma gargadin da shugaban Amurka Joe Biden ya yi.

Hukumomin Amurka da Birtaniya sun ce sun yi imanin cewa yiwuwar Mista Putin na aiwatar da wadannan barazanar babu tabbas.

Rikicin da ya yi tsami tsakanin Amurka da Rasha ya kara tabarbarewa tun bayan mamayar Ukraine.

Shugabannin kasashen biyu sun yi wata ganawa a tsakiyar shekarar 2021, wanda aka bayyana a matsayin wani mataki mai kyau na kyautata alaka.

Amma wannan ci gaban ya tsaya bayan da tashe-tashen hankula suka yi kamari a Ukraine.

Tun bayan mamayar dai babu wata tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen Amurka da Rasha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenMamayaRashaUkraineVladimir PutinYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

Next Post

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

13 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

17 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

19 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.