ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
4 years ago
Gine-gine

Wani abu mai tayar da hankali a bangaren gine-gine a Nijeriya a wannan lokacin yanzu wanda a lokutan-baya sai dai a ji labari dai-dai amma yanzu al’amarin ya zama ruwan dare, shi ne annobar rushewar gine-gine, wanda hakan ke nuna irin matsalar da bangaren gine-gine na Nijeriya ya shiga.

Rahotanni daga sassan kasar nan suna nuna yadda ake samun rugujewar gine-gine abin da ke kai ga asarar rayukar al’umma da dukiyoyin mutane da dama, mutane sun zura ido ga gwamnagti don ta samu musu mafita na yadda masu ruwa da tsaki da harkar gine-gine za su tabbatar da bin doka da oda a harkokinsu.

  • DA DUMI-DUMI: Wani Gini Mai Hawa 7 Ya Rushe A Legas

Zuwa yanzu rushewar gine-ginen da aka samu a baya ba mu ji labarin gwamnati ta dauki matakin hukunta masu hannu a kan faruwar lamarin ba, da kuma jami’an gwamnati wadanda su ke bayar da izinin yin gine-ginen da kaya marasa inganci.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, a watan Satumba, mutum biyu sun mutu yayin da ma’aikata 4 suka makale a karkashin baraguzai a yayin da wani bene mai hawa 2 ya rushe a unguwar Oba Abiodun Oniru a yankin rukunin gidaje na Oniru, a Lekki ta Jihar Legas.

Yakamata ya yi a lura da cewa, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, ta bayyana cewa, gidaje 30 suka rushe a sassa daban-daban na Jihar Legas a tsakanin watan Janairu zuwa Yuli na 2022.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Kididdiga ta baya bayan nan, kamar yadda Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, Dakta Femi Oke-Osanyitolu ya nuna, ya ce, daga cikin kiran gaggawa 973 da aka yi musu mafi yawa na rugujewar gine-gine ne, an kuma fi samun wadannan kiraye-kiraye na gaggawan ne daga karamar hukumar Alimosho inda aka samu gidaje 24 da suka ruguje gaba daya da gidaje 6 da wani bangare nasu ya ruguje da kuma wani gida da yake dab da rushewa.

Hakanan kuma, rahotanni daga kafafen watsa labarai na nuna cewa, akalla mutum 84 suka rasa rayukansu a cikin gidaje 18 da suka rushe a Jihar Legas a cikin shekara 2 da suka wuce.

Kusan mako 4 kenan da rushewar wani bene mai hawa 4 a yankin Bodija da ke Ibadan a Jihar Oyo sai kuma gashi wani bene mai hawa 2 ya sake rushewa a yankin da ake magana a daren ranar Lahadin da ta wuce.

A watan da ya gabata, wani bene mai hawa 4 ya rushe a Uyo, babbar birnin Jihar Akwa Ibom inda mutane da dama suka makale a cikin baraguzan ginin.

A watan Agusta kuma, wani mutum ya mutu bayan da wani bene mai tsawo ya rushe a garin Kano inda wasu da dama suka makale. An tabbatar da mutuwar mutum biyu a watan Agusta a yayin da wani bene mai hawa 3 ya rushe a garin Kubwa da ke yankin babban birnin tarayya Abuja.

A ra’ayin wannan jaridar, muna iya cewa, a halin yanzu muna fuskantar annobar rushewar gine-gine ne a kasar nan. Abin takaicin kuma shi ne, daga shekarar 1974 zuwa watan Yuli na shekarar 2021, kididdiga ta nuna cewa, gidaje 461 suka rushe a Nijeriya inda fiye da mutum 1,090 suka mutu wasu kuma suka rasa rayukansu.

A ‘yan shekarun nan an samu rushewar gini 295 a Jihar Legas, Abuja 16, Oyo, 16, Anambra 15, Kano 9, Ondo 10, Abia 9, Kwara 8, Ribers 8, Delta 8, Enugu 7, Ogun 7, Plateau 6, Kaduna 6, Edo 6, Imo 5, Osun 5, Benue 3, Adamawa 3, a Jihar Ebonyi kuma guda 3. An samu rushewar gini 2 a Neja, Kebbi 2, Ekiti 2, Cross Riber 2, Sokoto 1, Bauchi 1, Akwa-Ibom, Kogi 1, Jihar Katsina kuma gini 1.

Masana sun dora alhakin yawan rushewar gine-ginen kan yadda ake amfani da kayan aiki marasa inganci da rashin bin ainihin taswirar da aka samar don ginin da kuma rashin yin binciken da ya kamata a a kan yanayin kasar da za a yi ginin a kai, bugu da kari kuma amfani da baragurbin ma’aikata wadanda ba su da kwarewar da ta kamata na haifar da irin wannan matsalar ta rushewar gine-gine.

Muna kira da gwamnati da a tabbatar da an gano tare da hukunta dukkan kwararrun da ke da hannu a gidajen da suka rushe da wadanda suka zuba jari a harkar ginin da ya rushe, wannan zai zama darasi ga masu daukar aikin da ya rataya a kan da muhimmanci.

Ya kuma kamata gwamnati ta tabbatar da bin dokoki da ka’idojin da ke tattare da gine-gine a Nijeriya tare da hukunta duk wani jami’in da aka samu yana sakosako da ayyukansa wanda hakan ya kai ga rushewar gini a fadin tarayyar Nijeriya.

Gine-gine
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.