• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nnamdi Kanu Ya Nemi Diyyar Biliyan 100 Kan Ci Gaba Da Tsare Shi Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Nnamdi Kanu Ya Nemi Diyyar Biliyan 100 Kan Ci Gaba Da Tsare Shi Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu, ya shigar da karar gwamnatin tarayya a gaban kotu kan ci gaba da tsare shi da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ke yi.

A karar da aka shigar a babban kotun tarayya da ke Abuja, Kanu na neman a gaggauta sakin sa daga hukumar DSS tare da biyansa diyyar Naira biliyan 100 saboda tauye hakkinsa na ‘yanci da mutuncin dan Adam.

  • Ana Zargin Wani Mahaifi Da Karya Hannun Jaririnsa Saboda Yana Damunsa Da Kuka
  • Rashin Tsaro: Amurka Ta Umarci Jami’anta Su Fice Daga Abuja

Kanu ya ce karar ta zama dole ne biyo bayan gazawar gwamnatin tarayya na yin biyayya ga hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a ranar 13 ga Oktoba, wanda ya yi watsi da tuhumar ta’addancin da ake yi masa.

Kotun, wadda Mista Mike Ozekhome, SAN, ya shigar a madadin Kanu, mai kwanan wata 21 ga Oktoba na dauke da kara mai lamba FHC/ABJ/CS/1945/2022.

Kanu ya ce an yi shari’ar ne bisa tanadin kundin tsarin mulkin 1999.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

“Saboda sashe na 46 (1) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 da doka ta 1 da ta 2(1) na Dokokin Hakki (Tabbatar da Hukunci), duk mutumin da aka yi zargin cewa wani daga cikin tanade-tanaden na 4 na kundin tsarin mulkin kasar da ya ke, wanda yake da hakkin, ko ya kasance, ko kuma ana iya cin karo da shi a kowace jiha dangane da shi, na iya neman babbar kotun jihar domin ta yi masa hukunci.”

A cikin karar, Kanu yana son a bayyana cewa ci gaba da tsare shi da gwamnati ke yi daga ranar 13 ga Oktoba zuwa yau, ba daidai ba ne, zalunci, rashin sanin ya kamata ne, kuma ba bisa ka’ida ba.

“Ya keta hakkina na mutunta bil Adama, ‘yancin kai kamar yadda sashe na 34, 35, 36, 39, da 41 na kundin tsarin mulkin 1999 ya tabbatar.

Kanu kuma ya nemi a umarci wadanda ake kara da su sake shi daga hannunsu ba tare da wani sharadi ba.

Ya sake neman a hana wadanda ake kara shiga hakkinsa ko mu’amala da shi ta hanyar da ta dace da hakkinsa na asali da kundin tsarin mulki na 1999 ya ba shi.

Bugu da kari, yana neman a biya shi diyyar Naira biliyan 100 ga wadanda ake kara saboda tauye masa hakkinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiyafaraDiyyar Naira Biliyan 100DSSGwamnatin TarayyaKotuNnamdi KanuTsarews
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Wani Mahaifi Da Karya Hannun Jaririnsa Saboda Yana Damunsa Da Kuka

Next Post

Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

19 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

1 day ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

3 days ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.