ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nnamdi Kanu Ya Nemi Diyyar Biliyan 100 Kan Ci Gaba Da Tsare Shi Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi 

by Sadiq
4 years ago
Kanu

Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu, ya shigar da karar gwamnatin tarayya a gaban kotu kan ci gaba da tsare shi da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ke yi.

A karar da aka shigar a babban kotun tarayya da ke Abuja, Kanu na neman a gaggauta sakin sa daga hukumar DSS tare da biyansa diyyar Naira biliyan 100 saboda tauye hakkinsa na ‘yanci da mutuncin dan Adam.

  • Ana Zargin Wani Mahaifi Da Karya Hannun Jaririnsa Saboda Yana Damunsa Da Kuka
  • Rashin Tsaro: Amurka Ta Umarci Jami’anta Su Fice Daga Abuja

Kanu ya ce karar ta zama dole ne biyo bayan gazawar gwamnatin tarayya na yin biyayya ga hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a ranar 13 ga Oktoba, wanda ya yi watsi da tuhumar ta’addancin da ake yi masa.

ADVERTISEMENT

Kotun, wadda Mista Mike Ozekhome, SAN, ya shigar a madadin Kanu, mai kwanan wata 21 ga Oktoba na dauke da kara mai lamba FHC/ABJ/CS/1945/2022.

Kanu ya ce an yi shari’ar ne bisa tanadin kundin tsarin mulkin 1999.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

“Saboda sashe na 46 (1) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 da doka ta 1 da ta 2(1) na Dokokin Hakki (Tabbatar da Hukunci), duk mutumin da aka yi zargin cewa wani daga cikin tanade-tanaden na 4 na kundin tsarin mulkin kasar da ya ke, wanda yake da hakkin, ko ya kasance, ko kuma ana iya cin karo da shi a kowace jiha dangane da shi, na iya neman babbar kotun jihar domin ta yi masa hukunci.”

A cikin karar, Kanu yana son a bayyana cewa ci gaba da tsare shi da gwamnati ke yi daga ranar 13 ga Oktoba zuwa yau, ba daidai ba ne, zalunci, rashin sanin ya kamata ne, kuma ba bisa ka’ida ba.

“Ya keta hakkina na mutunta bil Adama, ‘yancin kai kamar yadda sashe na 34, 35, 36, 39, da 41 na kundin tsarin mulkin 1999 ya tabbatar.

Kanu kuma ya nemi a umarci wadanda ake kara da su sake shi daga hannunsu ba tare da wani sharadi ba.

Ya sake neman a hana wadanda ake kara shiga hakkinsa ko mu’amala da shi ta hanyar da ta dace da hakkinsa na asali da kundin tsarin mulki na 1999 ya ba shi.

Bugu da kari, yana neman a biya shi diyyar Naira biliyan 100 ga wadanda ake kara saboda tauye masa hakkinsa.

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.