• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Wani Mutum Da Katin Zabe Sama Da 100 A Sakkwato 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Wani Mutum Da Katin Zabe Sama Da 100 A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda a Jihar Sakkwato sun cafke wani mutum da ke da katin zabe sama da 100, watanni hudu kafin fara zaben 2023. 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Muhammed Ussaini Gumel ne, ya bayyana haka a ranar Alhamis yayin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Sokoto.

  • Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi
  • Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

Duk da cewa har yanzu hukumar ‘yansanda ba ta gano ainihin wadanda suka mallaki na’urar katin zaben ba, Gumel ya ce ana kyautata zaton masu wannan katin ba mazauna Sabon Birnin ba ne kadai inda aka kama wanda ake zargin.

Ya kuma yi kira ga jama’a musamman wadanda katinan zabensu ya bata, da su ziyarci hedikwatar hukumar inda za a duba katunan domin masu su su karbi abun su.

A cewarsa, an gurfanar da wanda ake zargin ta hanyar hujjoji da shaidun masu mallakar da suka fito a hedikwatar ‘yansanda don neman katinansu.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Jim kadan bayan kammala taron, kwamishinan ya kuma yi wa wasu sabbin jami’ai shida da aka kara wa karin girma ado da sabbin mukamai.

A halin da ake ciki, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce ba ta buga katin zabe na ‘yan Nijeriya cikin masu rajistar masu kada kuri’a daga ranar 15 ga watan Janairu zuwa 31 ga Yuli, 2022.

Kwamishinan INEC na kasa, Festus Okoye, ne ya bayyana hakan a cikin shirin Siyasa na gidan talabijin na Channels a ranar Laraba.

Okoye ya ce, “Idan kai mai rijista ne, wato idan kana cikin ‘yan Nijeriya miliyan 84 da suka rigaya suka yi rajista, za ka iya bin diddigin bayananka a cikin rumbun adana bayananmu.

“Na biyu, idan kana daya daga cikin wadanda suka yi rajista da hukumar a ci gaba da yin rijistar masu kada kuri’a tsakanin ranar 28 ga watan Yunin 2021 zuwa ranar 14 ga watan Janairun 2022, za ka iya bin diddigin inda katin zabenka yake, ka karbe shi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaKatin ZabeRajistaSakkwato
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Next Post

Manufar Sin Ta Fadada Bude Kofa Ga Waje Za Ta Tallafawa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

6 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

1 day ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
Manufar Sin Ta Fadada Bude Kofa Ga Waje Za Ta Tallafawa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Manufar Sin Ta Fadada Bude Kofa Ga Waje Za Ta Tallafawa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.