• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

  • ‘Yandaba Sun Farwa Tawagar Atiku Farmaki, Mutum 74 Sun Jikkata Suna Asibiti A Borno

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Atiku
Wike da Sauran Gwamnonin G5 yayin da suka ziyarci takwaransu na jihar Bauchi, Gwamna Bala Muhammad Kauran Bauchi

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kasance Ta Farko Wajen Yawaitar Mutane Masu Hazaka A Duniya

Next Post

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

5 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

6 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.