• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Man Fetur

Karancin man fetur ya addabi Jihar Zamfara, wanda hakan ya haifar da tsadar rayuwa a Jihar yayin da ‘yan kasuwa ke korafin karancin man fetir da tsadar kayayyaki. 

Leadership ta rawaito cewa yawancin mazauna jihar a yanzu suna tafiya mai nisa a kafa saboda ba za su iya biyan kudin ababen hawa ba.

  • Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Mallam Yunusa wanda ya zanta da manema labarai, ya ce isa birnin Gusau ne daga garin Danba mai tazarar kilomita bakwai da kafa.

“Na gargadi dukkan ‘yan uwana da kada su sake fitowa a 2023 da sunan zaben kowa saboda ban ga wata ribar dimokuradiyya a Nijeriya ba, musamman a Jihar Zamfara,” in ji shi.

Yunusa ya koka da cewa shi dan fansho ne yana karbar Naira 7,500 kacal a kowane wata daga gwamnatin jihar bayan ya yi wa gwamnatin jihar hidima tsawon shekaru 35 ba tare da wata kyautatawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

“Yaya Nijeriya za ta gyaru yayin da masu hannu da shuni ke kara arziki yayin da talakawa ke kara talaucewa? Dimokuradiyya kenan? Kamar yadda ya tambaya.

Da aka tambaye shi game da sake fasalin kudin, sai ya ce, al’amuran masu wawure dukiyar Nijeriya ne, talakawa ba su damu da wannan batu ba saboda shugabannin sun san kansu.

A halin da ake ciki, a ziyarar da wakilinmu ya kai wasu manyan kasuwanni a Gusau, babban birnin jihar, ya gano cewa harkokin kasuwanci na tafiyar hawainiya ba tare da hada-hadar masu saye ba.

Galibin mazauna jihar sun kuma yi korafin cewa duk da karancin man fetur da ke ci gaba da addabar kasar, amma ga dukkan alamu Jihar Zamfara ce ta fi fama da matsalar kasancewar lamarin ya gurgunta duk wasu harkokin tattalin arzikin Jihar.

“Ta yaya gwamnatin jiha za ta yi ikirarin cewa tana gamsar da kowa yayin da jama’a a jihar ke mutuwa saboda yunwa,” kamar yadda ya koka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko haram
Manyan Labarai

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

Kasar Sin Ta Tsara Matakai 20 Na Inganta Ayyukan Kandagarki Da Shawo Kan Annobar Covid-19

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.