• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Mataimakiyar Shugaban Asusun bunkasa noma na kasa da kasa Katherine Meighan ta bayyana cewa, asusun ya taimaka wa wasu manoma a kasar nan da dala miliyan biyar.
Meighan ta ce, asusun ya bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gonarsu.

Mataimakiyar ta bayyana hakan ne lokacin wata ganawa ta musamamn da ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammad Mohmood Abubakar a Abuja wadda ta ce, asusun ya bayar da taimakon ne don tausaya wa manoman da iftila’in na ambaliyar ruwan ta shafa.

  • Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

“Mun bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata gonakinsu”.
Meighan ta jinjina wa gwamnatin kasar bisa zuba jarin da ta yi a harkar noma, musaman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma ci gaba da habaka fannin aikin nama a Nijeriya.

“A susun na kuma yin aikin kafada da kafada da gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke a cikin karkara”.

Ta kuma nuna jin dadinta bisa karin tallafin, musaman domin a kara habaka fannin aikin noma a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, asusun na kuma yin aikin kafada da kafada gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke karkara.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

A na sa jawabin ministan ya mika godiyasa a madadin gwamnatin tarayya a kan wannan tallafin kudaden, inda ya bayar da tabbacin cewa, gwamnatin za ta tabatar tallafin ya kai ga wadanda aka yi abin dominsu.

A wani labarain makamancin wannan kuwa, rahotannin da suka fito daga wasu jihohin kasar nan sun ce, iftila’in na ambaliyar ruwa ta kara janyo hauhawan farashin shinkafa da sauran amfanin gona.

An ruwaito wasu daga cikin manoman shugabanin kungiyar manoman masara sun sanar da cewa, mai yuwa farashin ya karu rashi, saboda da tsadar takin zamani da manoma suka fuskanta a daminar bana, inda suka yi kira ga sauran takwarorinsu kan su guje wa sayar da amfanin gonakarsu bana domin gudun kauwace wa faskantar matsala.

Sun yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar, gwamnatocin kasar nan, musamman gwamnatin tarayya da kawo masu dauki, musamman domin kar su durkushe a cikin fannin.

An ruwaito cewa, a yanzu haka dai a wasu kasuwannin da ke a kasar nan, musaman a jihar kaduna, buhun shinkafa mai nauyin kilo 100 ana sayar da shi naira 19,000 21,000.

Sai dai, kuma, farashin buhun waken soya ana sayar da shi kan naira 22,000 zuwa naira 24,000, inda buhun masara ya kai nira 16,000, kuma buhun farin wake, ana samun sa a kan 44,000 saboda ba a shiga kakarsa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Faransa

Hukumar Zaɓe Ta Ce Babu Wani Binciken Laifi Da Suke Yi Wa Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.