ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Biyo bayan bala’in ambaliya da ta addabi al’umomi da dama a kasar nan a cikin ‘yan kwanakin nan, Masarautar Jordan ta hannun wata kungiyar agaji ta Jordan Hashemite, ta bai wa Nijeriya tallafin kayayyakin agaji iri-iri. 

Kayayyakin da aka bayar a karkashin umarnin Sarki Abdullah na II bin Al-Hussein Al Hashimi na Kasar Jordan da rundunar sojojin sama ta Royal Jordan ta kai wa gwamnatin tarayya sun hada da kunshin kayan abinci da tufafi da barguna da kayan tsaftar jiki.

  • “Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa
  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

A wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce wani jirgin saman Hercules C130 na rundunar sojojin sama na Masarautar Jordan da ke jigilar kayayyakin agajin ya isa bangaren dakon kaya na filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe, Abuja da misalin karfe 7: 45pm na daren Laraba.

ADVERTISEMENT

Da yake karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin tarayya, babban daraktan hukumar NEMA, Mustapha Habib Ahmed, ya yaba da irin wannan karamcin da Sarkin Jordan, da gwamnati da al’ummar Masarautar suka yi wa Nijeriya, musamman a halin da ake ciki a halin yanzu da ake ciki, don tallafa wa mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

Ahmed ya kuma mika godiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar Farouq bisa tallafin tare da bayar da tabbacin za a raba kayayyakin ga wadanda suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Mai magana da yawun tawagar da suka kai kayayyakin, Zeyed Mahmoud, ya ce sun dauki wannan mataki ne daga Sarkin Jordan domin tallafa wa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa, kuma ya kasance tare da hadin gwiwar kasa da kasa da Nijeriya kan wannan iftila’i kasancewar kasashen biyu ‘yan uwan ​​juna ne.

Wakilinmu ya tattaro cewa babban daraktan hukumar ta NEMA ya samu hadin kai da wasu daraktocin hukumar wajen karbar tallafin.

Haka kuma a filin jirgin akwai jami’an hukumar Kwastam da hukumar shige da fice ta kasa (NIS) da sauran hukumomin da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.