ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Biyo bayan bala’in ambaliya da ta addabi al’umomi da dama a kasar nan a cikin ‘yan kwanakin nan, Masarautar Jordan ta hannun wata kungiyar agaji ta Jordan Hashemite, ta bai wa Nijeriya tallafin kayayyakin agaji iri-iri. 

Kayayyakin da aka bayar a karkashin umarnin Sarki Abdullah na II bin Al-Hussein Al Hashimi na Kasar Jordan da rundunar sojojin sama ta Royal Jordan ta kai wa gwamnatin tarayya sun hada da kunshin kayan abinci da tufafi da barguna da kayan tsaftar jiki.

  • “Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa
  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

A wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce wani jirgin saman Hercules C130 na rundunar sojojin sama na Masarautar Jordan da ke jigilar kayayyakin agajin ya isa bangaren dakon kaya na filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe, Abuja da misalin karfe 7: 45pm na daren Laraba.

ADVERTISEMENT

Da yake karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin tarayya, babban daraktan hukumar NEMA, Mustapha Habib Ahmed, ya yaba da irin wannan karamcin da Sarkin Jordan, da gwamnati da al’ummar Masarautar suka yi wa Nijeriya, musamman a halin da ake ciki a halin yanzu da ake ciki, don tallafa wa mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

Ahmed ya kuma mika godiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar Farouq bisa tallafin tare da bayar da tabbacin za a raba kayayyakin ga wadanda suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Mai magana da yawun tawagar da suka kai kayayyakin, Zeyed Mahmoud, ya ce sun dauki wannan mataki ne daga Sarkin Jordan domin tallafa wa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa, kuma ya kasance tare da hadin gwiwar kasa da kasa da Nijeriya kan wannan iftila’i kasancewar kasashen biyu ‘yan uwan ​​juna ne.

Wakilinmu ya tattaro cewa babban daraktan hukumar ta NEMA ya samu hadin kai da wasu daraktocin hukumar wajen karbar tallafin.

Haka kuma a filin jirgin akwai jami’an hukumar Kwastam da hukumar shige da fice ta kasa (NIS) da sauran hukumomin da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.