ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

by Sadiq
4 years ago
Ambaliyar Ruwa

Biyo bayan bala’in ambaliya da ta addabi al’umomi da dama a kasar nan a cikin ‘yan kwanakin nan, Masarautar Jordan ta hannun wata kungiyar agaji ta Jordan Hashemite, ta bai wa Nijeriya tallafin kayayyakin agaji iri-iri. 

Kayayyakin da aka bayar a karkashin umarnin Sarki Abdullah na II bin Al-Hussein Al Hashimi na Kasar Jordan da rundunar sojojin sama ta Royal Jordan ta kai wa gwamnatin tarayya sun hada da kunshin kayan abinci da tufafi da barguna da kayan tsaftar jiki.

  • “Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa
  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

A wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce wani jirgin saman Hercules C130 na rundunar sojojin sama na Masarautar Jordan da ke jigilar kayayyakin agajin ya isa bangaren dakon kaya na filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe, Abuja da misalin karfe 7: 45pm na daren Laraba.

ADVERTISEMENT

Da yake karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin tarayya, babban daraktan hukumar NEMA, Mustapha Habib Ahmed, ya yaba da irin wannan karamcin da Sarkin Jordan, da gwamnati da al’ummar Masarautar suka yi wa Nijeriya, musamman a halin da ake ciki a halin yanzu da ake ciki, don tallafa wa mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

Ahmed ya kuma mika godiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar Farouq bisa tallafin tare da bayar da tabbacin za a raba kayayyakin ga wadanda suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Mai magana da yawun tawagar da suka kai kayayyakin, Zeyed Mahmoud, ya ce sun dauki wannan mataki ne daga Sarkin Jordan domin tallafa wa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa, kuma ya kasance tare da hadin gwiwar kasa da kasa da Nijeriya kan wannan iftila’i kasancewar kasashen biyu ‘yan uwan ​​juna ne.

Wakilinmu ya tattaro cewa babban daraktan hukumar ta NEMA ya samu hadin kai da wasu daraktocin hukumar wajen karbar tallafin.

Haka kuma a filin jirgin akwai jami’an hukumar Kwastam da hukumar shige da fice ta kasa (NIS) da sauran hukumomin da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.