• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce zai ware Dala biliyan 10 domin magance matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku ya bayyana hakan ne a Ilorin, babban birnin Jihar Kwara a wajen kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar PDP na Arewa ta Tsakiya, wanda aka gudanar a dandalin Ilorin.

  • Yadda ‘Yan Majalisa Suka Bai Wa Hammata Iska A Saliyo
  • Matsalar Karancin Man Fetur Na Ci Gaba Da Ta’azzara A Legas

Tsohon mataimakin shugaban kasar nan, ya ce za a yi amfani da kudin ne wajen taimaka wa matasan Nijeriya wajen kafa kanana da matsakaitan masana’antu.

“Ina so in tabbatar muku da cewa rashin aikin yi da matasa ke fama da shi a duk fadin kasar nan ba a iya Jihar Kwara ko shiyyar Arewa ta Tsakiya ya tsaya ba, yawancin ku a nan ‘yan kasa da shekara 30 ne kuma yawancin ku a nan ba su da aikin yi ko sana’a. Za mu tabbatar da cewa a cikin shirin namu na yi alkawarin cewa zan ware Dala biliyan 10 don ganin an samar da ayyukan yi ga matasa a kananan da matsakaitan sana’o’i don ba ku dama da kuma tabbatar da cewa an samar muku da ayyukan yi.

“Ba mu zo nan don mu muku karya ba, mu iyayenku ne, muna son ku zama kamar yadda muke, za mu ba ku dama, za mu kawo ku, za mu tabbatar kun cimma burinku, ko mene ne. Babban burin ku, shi ya sa muke nan, kar ku sake zabar APC, ku zabi duk ‘yan takarar PDP a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

“Mun kuma yi alkawarin dawo da tsaro a duk fadin kasar nan, lokacin da suka zo sai suka ce za su magance matsalar rashin tsaro nan a watanni shida, amma me muke gani? abubuwan da ke faruwa,” in ji Atiku.

Dan takarar shugaban kasar ya bukaci ’yan Kwara da su zabi dukkan ‘yan takarar PDP a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku, wanda ya ce a ranar Laraba ne jam’iyyar ta kaddamar da kwamitin mata na PDP, ya kara da cewa ita ce ta farko a tarihin babbar jam’iyyar adawa.

Ya yaba wa al’ummar Jihar Kwara bisa yawan fitowar jama’a tare da gode musu bisa goyon bayan da suka samu da kuma tarbar da tawagar yakin neman zabensa suka yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuKwaraPDPYakin Neman ZabeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Turai Sun Fusata Da Matakin Amurka

Next Post

An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

5 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

10 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

11 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

12 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

24 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

1 day ago
Next Post
An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.