• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da shirin nan na Gwamnatin Tarayya na raba kuɗin tallafi ga mabuƙata mutum 5,428 a Jihar Neja.

 

Ministar ta ƙaddamar da shirin ne a Gidan Gwamnatin jihar da ke Minna a ranar Talata.

  • Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

A taron ƙaddamarwar, ta yi amfani da wannan damar ta jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar ta Neja kan ibtila’in ambaliyar ruwa da ya same su a kwanan baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Daga nan ta ba da shawara ga waɗanda za su ci moriyar shirin da su yi amfani da kuɗin tallafin ta hanyar da ta dace domin su inganta rayuwar su ta yau da kullum, sa’annan ta ce kuɗin za su taimaka wa waɗanda bala’in ambaliyar ruwan ya shafa wajen samun sauƙi.

Ministar Jinƙai
Minista Sadiya Umar Farouq tare da Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Ahmed Matane, da wasu masu cin moriyar shirin

Hajiya Sadiya ta ce: “Burin mu a Jihar Neja shi ne mu raba tallafin tsabar kuɗin ga gungu-gungun mabuƙata mutum 5,428 da aka samo daga yankunan ƙananan hukumomi 25 da ke faɗin jihar.

 

Ta bayyana cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari, ta hanyar tsarin da ya fito da shi na taimaka wa kowa da kowa a al’umma, ya ba da umarnin cewa a tabbatar kashi 70 cikin ɗari na masu cin moriyar wannan shirin su kasance mata ne, sannan sauran kashi 30 cikin ɗari kuma su kasance matasa ne.

 

“Haka kuma ya ba da umarnin cewa a ware aƙalla kashi 15 cikin ɗari na jimillar masu cin moriyar shirin su kasance ‘yan ƙasar nan ne masu buƙatu na musamman, wato irin su naƙasassu da kuma tsofaffi tukuf a jihar.

 

“Ana matuƙar fatar cewa waɗanda za su fara cin moriyar shirin za su yi amfani da wannan tallafi wajen inganta rayuwar su, su nemi arziki, su samar da guraben aikin yi, su ɗaga matsayin rayuwar su.”

 

Ministar ta kuma miƙa kayan abinci da waɗanda ba na abinci ba ga waɗanda ambaliyar ruwan nan ta shafa, sannan ta ba da tabbacin cewa gwamnati za ta ci gaba da agaza wa mabuƙata kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya umarta.

 

A taron, har ila yau, ministar ta ƙaddamar da shirin nan na tallafi na Gwamnatin Tarayya mai taken ‘Government Enterprise Empowerment Programme’ (GEEP) inda aka samu mutum 3,166 da za a ba bashi mara ruwa da ya kama tsakanin N50,000 zuwa N300,000 kowane mutum ɗaya.

 

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani-Bello, ya gode wa Gwamnatin Tarayya da ita kan ta ministar saboda waɗannan shirye-shirye na haɓaka tattalin arzikin ƙasa. A cewar sa, sama da mutum miliyan ɗaya ne aka tsamo daga ƙangin fatara a ƙasar nan ta hanyar su.

 

Sani-Bello, wanda ya samu wakilci daga Sakataren Gwamnatin Jihar Neja, Alhaji Ahmed Matane, ya yi kira ga ma’aikatar Harkokin Jinƙai, da ta Harkokin Mata da ta Aikin Gona da kuma ta Matasa da Wasanni da su riƙa bin diddigin waɗanda su ka ci moriyar shirye-shiryen haɓaka rayuwa da ke ƙarƙashin su domin su tabbatar da cigaba da kuma nasarorin da ake samu daga wannan lokaci zuwa wannan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Sabbin Takardun Kudin Da Aka Kaddamar

Next Post

Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Ranar Litinin Mai Zuwa

Related

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

1 hour ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

10 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

11 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

12 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

13 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

13 hours ago
Next Post
Sati 3 Masu Zuwa Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa

Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Ranar Litinin Mai Zuwa

LABARAI MASU NASABA

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.