• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Ƙasar Kanada

CGI Isah Jere Ya Ce Za A Kawar Da Tsaikon Da Ake Samu Wajen Samun Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
fasfo

Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris (a dama) yayin da yake taya Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola kaddamar da sabuwar cibiyar bayar da ingantaccen fasfo a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Ottawa, kasar Kanada

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da sabon ingantaccen fasfo da ake wa laƙabi da “enhanced e-passport” tare da buɗe ofishin da zai riƙa samarwa a Ottawa da ke yankin Ontario a ƙasar Kanada, domin bai wa ‘Yan Nijeriya mazauna ƙasar damar samun sabon fasfon mai matakai daban-daban.

Nijeriya dai tana daga cikin ƙasashe biyar na duniya kuma ta farko a Afirka da suka samar da sabon ingantaccen fasfon. Shi dai sabon fasfon, an tsara shi ne da fasahohin zamani tare da inganta tsaro a cikinsa da kuma ƙara yawan samfuransa ciki har da mai shafi 64 da ke aiki har na tsawon shekara 10 domin ƙara kyautata walwalar ‘Yan Nijeriya masu balaguro a ƙasashen duniya.

  • Kayan Angonci Sun Yi Batan Dabo, An Sace Sadakin Amarya A Taron Daurin Aure A Kano

Sakamakon tsaron da aka ƙara a sabon fasfon ta fuskoki 25 fiye da wanda ake amfani da shi a yanzu, maɓarnata da masu satar shaida ba za su iya amfani da shi ba wajen damfara.

Da yake jawabi a yayin ƙaddamarwar, Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris, ya bayyana cewa duk da fara bayar da sabon ingantaccen fasfon a Kanada, za a ci gaba da bayar da tsohon da sabon a tare har zuwa lokacin da za a kammala aikin fasfunan da aka nema a baya.

“Za a ci gaba da bayar da sabon ingantaccen fasfon da kuma wanda ake bayarwa kafin zuwan sabon har sai lokacin da aka mayar da ɗaukacin cibiyoyin bayar da fasfo zuwa na sabon da aka samar”, ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Fasfo
CGI Isah Jere (na biyu a dama) yayin da Ministan Cikin Gida Aregbesola yake miqa wa Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Asekun sabon ingantaccen fasfon da aka kaddamar

Har ila yau, CGI Isah Jere ya ce za a magance tsaikon da ake samu wajen yi wa mutane fasfo matuƙar masu nema suna bin matakai da ƙa’idojin da aka shimfiɗa ta hanyar tabbatar da cewa sun gabatar da buƙatarsu ta fasfo ta shafin intanet tare da biyan kuɗi ta nan, da daidaita bayanan fasfonsu su yi daidai da bayanan da ke ƙunshe a katinsu na shaidar ɗan ƙasa (NIN).

Isah Jere ya ƙara jaddada cewa NIS za ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta sauke nauyin da tsarin mulkin ƙasa ya ɗora mata tare da kyautata mu’amala da abokan hulɗa a ko ina cikin faɗin duniya.

A nashi jawabin tun da farko, Ministan Cikin Gida, Rauf Ogbeni Aregbesola, ya bayyana cewa sakamakon ƙaddamar da ofishin sabon fasfon a Kanada, a halin yanzu ‘Yan Nijeriya mazauna can za su iya shiga shafin NIS na intanet su gabatar da buƙatunsu na fasfo kai-tsaye.

  • Daga Yanzu Wajibi Ne A Koyar Da Yara Da Harshen Gado A Firamare – Gwamnati

Ya ce, wa’adin da aka ɗiba ga mai neman sabon fasfo shi ne za a yi masa a cikin mako shida, yayin da wanda zai sabunta kuma za a yi masa a cikin mako uku. Waɗannan makonnin da aka ɗiba a cewar ministan, domin a bai wa NIS sarari ne ta yi bincike game da bayanan da mai neman fasfo ya gabatar da kuma tabbatar da ingancin aikin kamar yadda ake yi a duk ƙasashen duniya da suka ci gaba.

fasfo
Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris (a hagu), Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Adeyinka Asekun da Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola yayin kaddamarwar

Haka nan ya nanata muhimmancin daidaita bayanan fasfo da na katin ɗan ƙasa (NIN), domin a cewarsa, ana matuƙar samun matsala kan haka kuma da zarar an samu bambanci komai ƙanƙanta, za a samu tsaiko wajen aikin fasfon.

Wakazalika, da yake tofa albarkacin bakinsa, Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Adeyinka Asekun ya yaba wa Ministan da Kwanturola Janar na NIS bisa hoɓɓasar da suka yi wajen ƙaddamar da sabin ingantaccen fasfon a Kanada wanda ya ce ita ce ta uku da NIS ta samar da sabon fasfon baya ga Amurka da Ingila.

Ya shawarci ‘Yan Nijeriya da ke ƙasar su yi ƙoƙari su ci gajiyar wannan damar da NIS ta samar musu musamman wajen neman fasfo mai shafi 64 da ke aiki na tsawon shekara 10 wanda ake iya neman sabuntawa tun ana saura shekara ɗaya wa’adin aikinsa ya ƙare.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Nuna Takaicin Yadda Gwamnoni Ke Mayar Da Kauyuka Saniyar Ware

Next Post

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

6 hours ago
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
Labarai

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

7 hours ago
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu
Labarai

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

8 hours ago
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina
Labarai

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

10 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

12 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

13 hours ago
Next Post
Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.