ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Soki Gwamnoni Kan Karkatar Da Kudaden Kananan Hukumomi

by Abubakar Abba
3 years ago
Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari, ya soki gwamnonin kasar nan bisa karkatar da kudaden da ake tura wa kananan hukumomi da ke a daukacin fadin kasar.

Buhari ya yi wannan sukar ne a jawabinsa a gurin taron kwas na manyan jami’an cibiyar NIPSS karo na 44 na shekarar 2022, da ya gudana a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Da Dumi-Duminsa: Kotu Ta Tabbatar Da Adebutu A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Ogun
  • An Garkame Dalibin Da Ya Soki Aisha Buhari A Gidan Yari

Shugaban wanda ya sanar da hakan a yau Alhamis, ya bayyana cewa, kowa zai yi makakin yadda gwamnonin ke karbar kudade kananan hukumomin da ke a jihohinsu da sunansu, amma a karshe gwamnonin sai su rike su.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, irin wannan halin na gwamnonin ke kara haifar da cin hanci da rashawa a kasar nan.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wannan furucin na Buhari kan gwamonin, na zuwa ne bayan awa 24 da majalisar zartarwa ta kasa ta dora alhakkin karuwar talauci a kasar nan, musamman saboda gazawar gwamnonin wajen na bayar da ta su gudunmawar ta samar da ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Karamin ministan kudi da tsare-tsaren kasa, Clement Agba, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a jiya Laraba, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, hukumar kididdigar ta kasa NBS, a kwanan baya ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya miliyan 133 ne ke fama da talauci.

Agba ya sanar da hakan a martanin da ya mayar na tambayar da manema labarai suka yi masa na cewa, shi da ministar kudi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahmed wane kokari suke yi don a rage wa akasarin ‘yan Nijeriya radadin talaucin da suke fuskanta a yanzu.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta hanyar shirinta na samar da saukin rayuwa ga ‘yan Nijeriya, na ci gaba da zuba kudade domin a rage wa ‘yan Nijeriya halin kuncin ruwa da suke fuskanta, inda ya bayyana cewa, kashi 72 na talaucin da ake fuskanta, ana samun hakan ne a kananan hukumomi, saboda gwamnonin su, sun yi watsi da al’ummar da ke karkara.

Agba ya kara da cewa, akasarin gwamonin, sun karkatar da yin ayyukansu ne a birane, musamman wajen gina manyan gadoji, gyaran filin jirgin sama da kuma gudanar da wasu manyan ayyuka, maimakon mayar da hankulinsu wajen raya karkara da jama’a.

Ya shawarci gwamnonin da su mayar da hankulinsu wajen samar da shirye-shiyen da za su inganta rayuwar akasarin ‘yan Nijeriya, domin a tsamo su daga cikin radadin talaucin da suke fuskanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.