ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Soki Gwamnoni Kan Karkatar Da Kudaden Kananan Hukumomi

by Abubakar Abba
4 years ago
Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari, ya soki gwamnonin kasar nan bisa karkatar da kudaden da ake tura wa kananan hukumomi da ke a daukacin fadin kasar.

Buhari ya yi wannan sukar ne a jawabinsa a gurin taron kwas na manyan jami’an cibiyar NIPSS karo na 44 na shekarar 2022, da ya gudana a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Da Dumi-Duminsa: Kotu Ta Tabbatar Da Adebutu A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Ogun
  • An Garkame Dalibin Da Ya Soki Aisha Buhari A Gidan Yari

Shugaban wanda ya sanar da hakan a yau Alhamis, ya bayyana cewa, kowa zai yi makakin yadda gwamnonin ke karbar kudade kananan hukumomin da ke a jihohinsu da sunansu, amma a karshe gwamnonin sai su rike su.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, irin wannan halin na gwamnonin ke kara haifar da cin hanci da rashawa a kasar nan.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wannan furucin na Buhari kan gwamonin, na zuwa ne bayan awa 24 da majalisar zartarwa ta kasa ta dora alhakkin karuwar talauci a kasar nan, musamman saboda gazawar gwamnonin wajen na bayar da ta su gudunmawar ta samar da ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Karamin ministan kudi da tsare-tsaren kasa, Clement Agba, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a jiya Laraba, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, hukumar kididdigar ta kasa NBS, a kwanan baya ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya miliyan 133 ne ke fama da talauci.

Agba ya sanar da hakan a martanin da ya mayar na tambayar da manema labarai suka yi masa na cewa, shi da ministar kudi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahmed wane kokari suke yi don a rage wa akasarin ‘yan Nijeriya radadin talaucin da suke fuskanta a yanzu.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta hanyar shirinta na samar da saukin rayuwa ga ‘yan Nijeriya, na ci gaba da zuba kudade domin a rage wa ‘yan Nijeriya halin kuncin ruwa da suke fuskanta, inda ya bayyana cewa, kashi 72 na talaucin da ake fuskanta, ana samun hakan ne a kananan hukumomi, saboda gwamnonin su, sun yi watsi da al’ummar da ke karkara.

Agba ya kara da cewa, akasarin gwamonin, sun karkatar da yin ayyukansu ne a birane, musamman wajen gina manyan gadoji, gyaran filin jirgin sama da kuma gudanar da wasu manyan ayyuka, maimakon mayar da hankulinsu wajen raya karkara da jama’a.

Ya shawarci gwamnonin da su mayar da hankulinsu wajen samar da shirye-shiyen da za su inganta rayuwar akasarin ‘yan Nijeriya, domin a tsamo su daga cikin radadin talaucin da suke fuskanta.

Buhari
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.