• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

A safiyar yau Alhamis ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da shugaban majalisar zartaswa ta Turai Charles Michel a babban dakin taruwar jama’a da ke birnin Beijing.

Xi Jinping ya bayyana cewa, dangantakar da ke tsakanin Sin da Turai ta dade da ci gaba, wadda ta dace da muradun bangarorin biyu da na kasashen duniya. Game da ci gaban dangantakar, Xi ya gabatar da ra’ayoyi guda hudu, na farko shi ne tabbatar da sanin juna yadda ya kamata, na biyu shi ne warware sabane-sabane yadda ya kamata, na uku shi ne inganta hadin kansu, sai na hudu kyautata daidaituwa a tsakanin kasa da kasa.

  • Xi Jinping Ya Aikawa MDD Sakon Murnar Taron Tunawa Da Ranar Goyon Bayan Palasdinawa

A jawabinsa Michel ya nuna cewa, Tarayyar Turai tana fatan zama abokiyar hadin gwiwar Sin ta kwarai.

A yayin tattaunawar bangarorin biyu kan matsalar Ukraine, Xi ya bayyana matsayin kasar Sin, yana mai cewa, warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa na dacewa da moriyar kasashen Asiya da Turai.

Sannan a wajen taron manema labarai da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta shirya a yau Alhamis, yayin da take amsa tambayar da ta shafi hadin-gwiwar Sin da Turai a fannin tattalin arziki da kasuwanci, mai magana da yawun ma’aikatar Shu Jueting ta bayyana cewa, kasarta na maida hankali sosai wajen bunkasa alakarta da kasashen Turai, da dukufa kan zurfafa hadin-gwiwarsu ta cimma moriyar juna, a wani kokari na tabbatar da samar da isassun kayayyaki a duniya, da kiyaye zaman doka da oda ta fuskar tattalin arziki da kasuwancin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

Rahotannin sun ce, a karkashin jagorancin shugabannin bangarorin biyu, akwai alakar tattalin arziki mai karfi tsakanin Sin da Turai a halin yanzu. Daga watan Janairu zuwa Oktobar bana, jimillar kudin cinikayyar su ta kai dala biliyan 711.4, adadin da ya karu da kaso 6.3 bisa dari. Kasar Sin ita ce babbar abokiyar cinikayya ta farko ga kungiyar tarayyar Turai wato EU, yayin da EU din ke ci gaba da zama babbar aminiyar cinikayya ta biyu ga kasar ta Sin. (Safiyah Ma, Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Next Post
Kungiyar Mata ‘Yan Jarida Ta Yi Sabuwar Shugaba A Kebbi

Kungiyar Mata 'Yan Jarida Ta Yi Sabuwar Shugaba A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.