• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Gwamnonin Nijeriya 36 sun shaida wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, cewar gazawarsa wajen samar da tsaro da kuma kasa cika alkawuran da ya daukar wa ‘yan Nijeriya ne dalilan da suka jefa jama’ar kasar nan cikin halin kunci rayuwa da talauci.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnonin, Abdurazaque Bello-Barkindo, ya rabawa manema labarai, ta ce abin takaici ne yaddda gwamnatin tarayya ke neman dora wa gwamnonin laifi dangane da irin talauci da halin kuncin da mazauna yankunan karkarar kasar nan ke fama da su.

  • Sinawa Na Jimamin Rasuwar Jiang Zemin
  • Alkalai 15 Za Su Gurfana Gaban NJC Kan Zargin Aikata Rashin Da’a

Gwamnonin sun ce a 2019, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewar zai fitar da mutane miliyan 100 daga kangin talaucin da ya addabi jama’a, amma a yau alkaluma sun nuna cewar ‘yan Nijeriya sama da miliyan 130 ne ke fama da talauci, inda suke rayuwa kasa da Dala guda a kowace rana.

Sanarwar ta ce a karkashin gwamnatin Buhari, an kwashe watanni kamfanin man NNPC ba ya iya zuba ribar da yake samu a asusun gwamnati, abin da ya tilasta wa gwamnonin neman mafita ta wasu hanyoyi wajen samun kudaden shiga domin cike gibin kudaden da suke samu daga gwamnatin tarayya domin sauke nauyin da ke kansu a bangare noma da raya karkara da ayyukan jinkai da kuma kula da lafiyar jama’a.

Gwamnonin sun kuma caccaki ministan kasafin kudi, Clement Agba, wanda ya zargi gwamnonin da jefa mutane sama da kashi 72 a yankunan karkara cikin talauci da shara karya wajen kauda kan jama’a daga assalin abin da yake faruwa.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Sanarwar ta ce abin sani shi ne, aikin farko da ya rataya a kan gwamnatin tarayya, shi ne kare lafiya da kuma dukiyoyin jama’a wajen samar da tsaro, domin aiwatar da harkokin ci gaba, amma abin takaici gwamnatin tarayya ta gaza a wannan bangaren, inda ta bar ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda da kuma masu garkuwa da mutane suka mayar da kasar dandalin kashe jama’a da sace mutane a gidajensu da makarantu da kasuwanni da kuma gonaki.

Gwamnonin sun ce tabbas gazawar shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke jagorancin gwamnatin tarayya, ne ya haifar da dalilan kasa noma da samar da abinci da kuma harkokin kasuwaci a yankunan karkara, saboda yadda zaman lafiya ya gagara, abin da ya hana mutane zuwa gonakinsu da kuma kasuwanni.

Wannan martini na zuwa ne ya biyo bayan zargin da ministan kasafin kudi, Clement Agba, ya yi wa gwamnonin, inda ce sun mayar da hankali wajen gina gadodin sama da filayen jiragen sama, maimakon bunkasa rayuwar jama’ar karkara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.