• Leadership Hausa
Monday, January 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

by Sadiq
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

Gwamnonin Nijeriya 36 sun shaida wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, cewar gazawarsa wajen samar da tsaro da kuma kasa cika alkawuran da ya daukar wa ‘yan Nijeriya ne dalilan da suka jefa jama’ar kasar nan cikin halin kunci rayuwa da talauci.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnonin, Abdurazaque Bello-Barkindo, ya rabawa manema labarai, ta ce abin takaici ne yaddda gwamnatin tarayya ke neman dora wa gwamnonin laifi dangane da irin talauci da halin kuncin da mazauna yankunan karkarar kasar nan ke fama da su.

  • Sinawa Na Jimamin Rasuwar Jiang Zemin
  • Alkalai 15 Za Su Gurfana Gaban NJC Kan Zargin Aikata Rashin Da’a

Gwamnonin sun ce a 2019, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewar zai fitar da mutane miliyan 100 daga kangin talaucin da ya addabi jama’a, amma a yau alkaluma sun nuna cewar ‘yan Nijeriya sama da miliyan 130 ne ke fama da talauci, inda suke rayuwa kasa da Dala guda a kowace rana.

Sanarwar ta ce a karkashin gwamnatin Buhari, an kwashe watanni kamfanin man NNPC ba ya iya zuba ribar da yake samu a asusun gwamnati, abin da ya tilasta wa gwamnonin neman mafita ta wasu hanyoyi wajen samun kudaden shiga domin cike gibin kudaden da suke samu daga gwamnatin tarayya domin sauke nauyin da ke kansu a bangare noma da raya karkara da ayyukan jinkai da kuma kula da lafiyar jama’a.

Gwamnonin sun kuma caccaki ministan kasafin kudi, Clement Agba, wanda ya zargi gwamnonin da jefa mutane sama da kashi 72 a yankunan karkara cikin talauci da shara karya wajen kauda kan jama’a daga assalin abin da yake faruwa.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan 5 Da Zaku So Ku Ji A Ganawar Gwamnan CBN Da Shugaba Buhari A Daura

Inganta Ilimi: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Dauki Karin Sabbin Malamai 1,000 Aiki

Sanarwar ta ce abin sani shi ne, aikin farko da ya rataya a kan gwamnatin tarayya, shi ne kare lafiya da kuma dukiyoyin jama’a wajen samar da tsaro, domin aiwatar da harkokin ci gaba, amma abin takaici gwamnatin tarayya ta gaza a wannan bangaren, inda ta bar ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda da kuma masu garkuwa da mutane suka mayar da kasar dandalin kashe jama’a da sace mutane a gidajensu da makarantu da kasuwanni da kuma gonaki.

Gwamnonin sun ce tabbas gazawar shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke jagorancin gwamnatin tarayya, ne ya haifar da dalilan kasa noma da samar da abinci da kuma harkokin kasuwaci a yankunan karkara, saboda yadda zaman lafiya ya gagara, abin da ya hana mutane zuwa gonakinsu da kuma kasuwanni.

Wannan martini na zuwa ne ya biyo bayan zargin da ministan kasafin kudi, Clement Agba, ya yi wa gwamnonin, inda ce sun mayar da hankali wajen gina gadodin sama da filayen jiragen sama, maimakon bunkasa rayuwar jama’ar karkara.

Tags: AlkawariBuhariGwamnoniKarkaraMartaniNNPCTalauci
Previous Post

Sinawa Na Jimamin Rasuwar Jiang Zemin

Next Post

Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

Related

Abubuwan 5 Da Zaku So Ku Ji A Ganawar Gwamnan CBN Da Shugaba Buhari A Daura
Manyan Labarai

Abubuwan 5 Da Zaku So Ku Ji A Ganawar Gwamnan CBN Da Shugaba Buhari A Daura

1 day ago
Inganta Ilimi: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Dauki Karin Sabbin Malamai 1,000 Aiki
Manyan Labarai

Inganta Ilimi: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Dauki Karin Sabbin Malamai 1,000 Aiki

1 day ago
Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu
Manyan Labarai

Babu Wata Baraka Tsakanina Da Buhari – Tinubu

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Kasurguman ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Mutane 7, Sun Kwato 2.1m Kudin Fansa

2 days ago
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari
Manyan Labarai

Ba Don A Wahalar Da Talaka AKa Sauya Kudin Nijeriya Ba —Buhari 

2 days ago
Babu Barazanar Kai Hari A Kano – ‘Yansanda
Manyan Labarai

DPO Ya Yanke Jiki Ya Fadi, Ya Rasu A Jigawa

2 days ago
Next Post
Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

January 30, 2023
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

January 30, 2023
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

January 30, 2023
Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

January 30, 2023
Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

January 30, 2023
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

‘Yan Majalisar Tarayya 3 Na Jam’iyyar APC Sun Koma Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina

January 30, 2023
Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

January 30, 2023
DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

January 30, 2023
Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

January 30, 2023
Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

January 30, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.