• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Qatar 2022: ‘Yan Asalin Afirka Da Tauraruwarsu Ke Haskawa A Wasu Kasashe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A babban taron hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA karo na 70, wanda aka yi a watan Satumbar shekara ta 2020, mambobin hukumar sun amince da wani canji na damar buga wa kasashe wasa.

Sai dai kafin wannan lokacin, doka ta bayyana cewa duk dan wasan da ya bugawa kasa wasa guda daya ba zai sake zuwa wata kasar ya buga mata wasa ba har karshen rayuwar sa wanda a haka aka dade ana tafiya.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Sai dai a babban taron na FIFA karo na 70, an amince cewa idan dan wasa ya buga wasa daya zai iya canja kasar da yake so a gaba har sai idan wasa uku ya buga, hakan yana nufin idan dan wasa ya buga wa kasa wasa uku na wata gasar ba shi da damar zuwa wata kasar ya buga mata wasa.

A gasar cin kofin duniyar da a yanzu haka ake ci gaba da fafata wa a kasar Qatar, akwai ‘yan wasa da dama daga nahiyar Afirka da suke buga wa kasashen da bana Afirka ba:
Dan wasa Musab Kheder: Dan wasan baya, yana buga wa kasar Qatar wasa ne sai dai a birnin Khartoum na kasar Sudan aka haife shi kuma yana buga wasanninsa a kungiyar Al-Sadd ta kasar Qatar.

Ansu Fati: Shima zakakurin dan wasa ne wanda yake wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Spaniya sai dai an haife shi ne a kasar Guinea-Bissau kafin ya koma kasar Spain tun yana dan karamin yaro.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Alphonso Dabies: Matashin dan wasa wanda yake buga wasan sa a kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta kasar Jamus, dan wasan mai shekara 22 a duniya, yana buga wasa a tawagar kasar Canada amma kuma an haife shi ne a birnin Budurburam na kasar Ghana.

Eduardo Camabinga: Kwararren dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid kuma yana wakiltar kasar Faransa ne amma kuma an haife shi ne a sansanin ‘yan gudun hijira na Angola bayan da iyayensa suka gudu daga kasar Congo amma kuma ya girma a Faransa.

Youssoufa Moukoko: Dan wasa ne wanda yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Borrusia Dortmund dake kasar Jamus amma kuma an haife shi ne a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde kuma kawo yanzu yana da shekara 18 a duniya.

Danilo Pereeira: Dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German mai shekara 31 a duniya yana wakiltar kasar Portugal ne a wasannin kasashe amma kuma a kasar Guinea-Bissau aka haife shi.
Stebe Mandanda: Mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Rennes ta kasar Faransa yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar ta Faransa ne amma kuma an haife shi ne a Jamhuriyar Dimokradiyar Congo.

Breel Embolo: Dan wasan da a yanzu yake wakiltar kasar Switzerland a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wa kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta kasar Faransa, an haife shi a babban birnin kasar Kamaru wato Yaounde.

Mohammed Muntari: Mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a kasar Ghana amma kuma yana buga wasa a tawagar ‘yan wasan kasar Qatar tare da kungiyar kwallon kafa ta Al-Duhail dake Qatar.

Amadou Onana: Dan wasan mai shekara 28 a duniya an haife shi ne a babban birnin kasar Senegal wato Dakar amma yanzu yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Belgium ne a wasannin kasa da kasa kuma yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Eberton ta kasar Ingila.

William Cavalho: Dan wasan yana buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Real Betis ta kasar Spain kuma yana wakiltar tawagar ‘yan wasan kasar Portugal ne a wasannin kasa da kasa amma kuma a kasar Angola aka haife shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

1 day ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

4 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

4 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

6 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

6 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

7 days ago
Next Post
FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

FIFA Za Ta Hukunta ‘Yan Wasan Uruguay Hudu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.